Najeriya @64: Muhimman Abubuwa 7 daga Jawabin Tinubu na Ranar Samun 'Yanci

Najeriya @64: Muhimman Abubuwa 7 daga Jawabin Tinubu na Ranar Samun 'Yanci

  • Jawabin shugaban kasa Bola Tinubu na ranar samun ‘yancin kai a 2024 ya nuna tsayin daka da ci gaban da al’ummar kasar ke samu
  • Muhimman batutuwa daga jawabinsa sun haɗa da sauye-sauyen tattalin arziki, ci gaban tsaro, da kuma shirye-shiryen ƙarfafa matasa
  • Jawabin Tinubu na ranar 'yanci ya nuna aniyar hadin kan kasa da kuma kyakkyawar makoma ga daukacin ‘yan Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Yayin da Najeriya ke cika shekaru 64 da samun 'yancin kai, al'ummar kasar sun cika da murna da kuma jinjinawa 'yan mazan jiya da suka tabbatar da 'yancin.

Fadi tashin da aka yi daga ranar 1 ga Oktoba, 1960 zuwa yau, na cike da nasarori da kuma kalubale. Sai dai kuma, gumin magabatanmu bai zuba kasa a banza ba.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da murnar ranar ƴanci: Gwamnatin tarayya ta karawa ƴan fansho albashi

Shugaba Bola Tinubu ya yi jawabi kai tsaye a ranar 'yancin Najeriya
Abubuwa 7 daga jawabin ranar 'yanci da Tinubu ya gabatar. Hoto: @DOlusegun
Asali: Twitter

Jawabin murnar 'yancin kan Najeriya

Jawabin ranar samun ‘yancin kai na bana da Bola Tinubu ya yi, ya nuna harsashin da aka sanya domin ci gaban kasar a gaba, kamar yadda Olusegun Dada ya wallafa a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jawabin nasa ya tabo batutuwa masu muhimmanci kamar sauye-sauyen tattalin arziki, tsaro, bunkasa aikin gona, sauye sauyen makamashi, karfafa matasa, da hadin kan kasa.

Ga muhimman abubuwa guda bakwai daga jawabin ranar samun ‘yancin kai na shugaba Tinubu a 2024:

1. Waiwaye kan shekarun 'yanci

Shugaba Bola Tinubu ya fara jawabinsa ne da yin tsokaci kan fadi tashin Najeriya a shekaru 64 da kasar ta yi tun bayan samun ‘yancin kai.

Duk da tarin kalubale, ya ce kasar ba ta nuna gazawa ba sakamakon hadin kan 'yan kasar, inda ya bayyana Najeriya a matsayin kasa mai karfi da cikakken iko.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Ana murnar samun ƴanci, gwamna ya ƴanta fursunoni a Najeriya

2. Gyaran tattalin arziki

Shugaba Tinubu ya bayyana gagarumin garambawul na tattalin arziki da gwamnatin tarayyar ta ke yi da nufin rage radadin wahala da inganta rayuwa.

Musamman ma, ya ce gwamnatinsa ta jawo hannun jarin sama da dala biliyan 30 daga kasashen waje a cikin shekarar da ta gabata.

Kazalika, gwamnatinsa ta biya dala biliyan bakwai da kuma sama da Naira tiriliyan 30 na wasu basussukan cikin gida da waje.

3. Samar da tsaro da yakar ta'addanci

Shugaban ya nuna alfahari da cewa an samu ci gaba a yaki da ta'addanci da 'yan fashin daji a Najeriya.

Sama da kwamandojin ‘yan Boko Haram 300 ne aka kashe, lamarin da ya maido da zaman lafiya a daruruwan garuruwan Arewa tare da ba dubban mutane damar komawa gida.

4. Cigaban harkar noma

Gwamnatin Tinubu na samun cigaba a harkar noma ta hanyar saka hannun jari a harkar noma na zamani.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Ahmadu Bello da wasu mutane 9 da suka yi fafutukar samun ‘yanci

Manoma na karbar taki da taraktoci, kuma an shirya kafa wata cibiyar hada taraktocin John Deere 2,000 da sauran kayan aikin gona.

5. Sauye sauyen makamashi

Kokarin shugaban kasa a kan iskar gas din CNG domin ganin ya isa lungu da sakon kasar nan ya na ci gaba da tabbata.

Gwamnatin Tarayya tana kuma taimaka wa jihohi wajen samun motocin CNG domin sufurin jama'a cikin farashi mai rahusa.

6. Tallafawa matasa

Wani babban abin jan hankali a jawabin shi ne sanarwar taron matasa na kasa na kwanaki 30 domin magance kalubale da damarmakin da matasan Najeriya ke fuskanta.

An samar da shirin 3MTT domin samar da kwararrun matasa kan fasa a kasar, yayin da asusun ba da lamunin karatu (NELFUND) ke ba da rancen kudi ga ɗalibai.

7. Hadin kan kasa da zaman lafiya

Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da hadin kan kasa da dorewar kyakkyawar zamantakewa.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya kare manufofin gwamnati, ya jaddada alfanun cire tallafin fetur

Ya kuma jaddada mahimmancin kasuwanci da saukin gudanar da shi, tare da karfafa gwiwar ‘yan Najeriya da su jajirce a kan ci gaban kasar domin samun kyakkyawar makoma.

Jagororin neman 'yancin kai a Najeriya

Tun da fari, mun ruwaito cewa daga Abubakar Tafawa Balewa zuwa Nnamdi Azikiwe, mutane da dama sun sadaukar da rayukansu domin 'yancin Najeriya.

A yayin da Najeriya ke murnar cika shekaru 64 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka, Legit Hausa ta tattaro bayanin jagorori 10 da suka nemawar kasar 'yanci.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.