N70,000: Jerin Gwamnonin Arewa da ke Shirin Fara Karin Albashi

N70,000: Jerin Gwamnonin Arewa da ke Shirin Fara Karin Albashi

  • Wasu gwamnonin Arewa sun yi alkawarin fara biyan mafi ƙarancin albashi zuwa N70,000 da zarar gwamnatin tarayya ta fara
  • A makon da ya wuce gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta fara biyan ma'aikata mafi ƙarancin albashi na N70,000
  • A wannan rahoton, mun tatttaro muku jerin gwamnonin Arewa da suka yi alkawarin fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Arewa - Wasu gwamnonin Arewa sun dauki alkawarin fara biyan sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikata.

Gwamnonin sun yi alkawarin fara karin albashin ne da zarar gwamnatin tarayya ta yiwa ma'aikata kari.

Gwamnonin Arewa
Jerin gwamnonin dasuka yi alkawrin karin albashi. Hoto: Abdul No Shaking
Asali: Facebook

A wannan rahoton, mun tatttaro muku jerin gwamnonin Arewa da suka yi alkawarin fara karin albashi.

Kara karanta wannan

Za a biya ma'aikata N930,000 a shekara? an fadi tsarin biyan sabon albashin N70,000

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnonin da suka yi alkawarin karin albashi

1. Gwamnan Nasarawa

Punch ta ruwaito cewa gwamnatin jihar Nasarawa ta bayyana cewa a shirye ta ke domin yiwa ma'aikata karin albashi.

A kwanakin baya ne hadimin gwamna Abdullahi Sule, Peter Ahemba ya ce gwamnan yana jiran gwamnatin tarayya ne ta fara karin albashi.

2. Gwamnan Sokoto

Gwamnan Sokoto ya bayyana cewa gwamnatinsa tana shirye domin fara biyan ma'aikata N70,000.

Ahmed Aliyu ya ce gwamnatinsa tana kan shirye shiryen karin albashin ma'aikata a jihar Sokoto zuwa N70,000.

3. Gwamnan Gombe

Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya ce gwamnatinsa ba za ta yi wasa wajen karin albashi ba.

Legit ta ruwaito cewa gwamna Inuwa Yahaya ya ce yana jiran gwamnatin tarayya ne ta fara karin albashi ga ma'aikata.

Sauran gwamnoni kan karin albashi

Gwamnonin jihohin Kebbi, Katsina, Taraba, Kogi da Kano duk sun yi alkawarin karin albashi ga ma'aikata.

Kara karanta wannan

Daga ƙarshe, Tinubu ya fara biyan ma'aikata sabon albashin N70,000

Haka zalika gwamnan Zamfara ya ce zai fara biyan sabon albashi da zarar kwamiti sun kammala aikinsu.

Gwamnan Adamawa ya fara biyan sabon albashi yayin da kallo ya koma kan gwamnonin da suka yi alkawrin fara biyan N70,000 bayan gwamnatin tarayya.

Anambra: Gwamna zai yi karin albashi

A wani rahoton, kun ji cewa gwamna Chukwuma Soludo ya sanar da cewa zai fara biyan ma'aikatan jiharsa ta Anambra sabon albashin N70,0000 a watan Oktoba.

Gwamnan Chukwuma Soludo ya bayyana hakan ne a yayin ganawa da dukkanin shugabannin makarantun firamare da sakandare a Awka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng