Bayan Tantancewar Sanatoci, Tinubu Ya Rantsar da Sabuwar Shugabar Alkalan Najeriya

Bayan Tantancewar Sanatoci, Tinubu Ya Rantsar da Sabuwar Shugabar Alkalan Najeriya

  • A ranar Litinin, 30 ga watan Satumbar 2024 ne shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da shugabar alkalan Najeriya ta 23
  • An rahoto cewa Tinubu ya rantsar da Kudirat Kekere-Ekun a matsayin shugabar alkalan a zauren majalisar zartarwar tarayya
  • Kekere-Ekun ta sha alwashin zamantar da fannin shari'ar kasar inda ta ce za a rika gudanar da shari'o'in ta'addanci ta yanar gizo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Kudirat Kekere-Ekun a matsayin shugabar alkalan Najeriya (CJN).

An gudanar da bikin rantsuwar ne a zauren majalisar zartarwar tarayya da ke Aso Rock Villa a ranar Litinin bayan da majalisar dattawa ta amince da nadin a makon jiya.

Kara karanta wannan

Rigima ta barke da dattawa suka kalubalanci gwamna kan nadin sabon sarki

Tinubu ya ranstar da Kekere-Ekun matsayin shugabar alkalan Najeriya
Tinubu ya rantsar da Kekere-Ekun matsayin shugabar alkalan Najeriya ta 23. Hoto: @NGRPresident
Asali: Twitter

An ranstar da shugabar alkalai

Jaridar The Cable ta rahoto cewa Kekere-Ekun ce shugabar alkalan Najeriya ta 23 kuma mace ta biyu da ta rike wannan mukami a tarihin kasar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakazalika, an ce an Kekere-Ekun ta kasance a ofishin a matsayin mukaddashiya bayan ritayar Olukayode Ariwoola a watan Agusta.

A yayin zaman tantance nadin da aka yi a zauren majalisar dattawa, shugabar alkalan ta amsa tambayoyi kan sauye-sauyen da take fatan aiwatarwa a bangaren shari’a.

"Zan tabbatar an zamanantar da fannin shari'a. Za mu kawo sauki wajen bibiyar shari'o'i da kuma tsawatar da alkalai idan suna wasa da ayyukansu."

- A cewar Kekere-Ekun.

Za a zamantar da fannin shari'a

Musamman a shari'o'in aikata laifuka, shugabar alkalan ta ta ce za a rika zaman shari'ar a yanar gizo idan har aka fahimci za a samu tsaiko a zaman kotun zahiri.

Kara karanta wannan

Cin hancin N15m: Majalisar wakilai ta gayyaci shugaban EFCC da wasu mutum 2

“Muna nazarin hanyoyin da za mu tabbatar da cewa ana yawan rage cunkoso a gidajen yari.
"Za a rika zaman shari'ar ta yanar gizo, rashin gabatar da wadanda ake tuhuma a gaban kotu shi ke kawo jinkirin shari'o'in aikata laifuffuka."

- A cewar shugabar alkalan.

Tinubu ya nada shugabar alkalai

Tun da fari, mun ruwaito cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada sabuwar shugabar alkalan Najeriya (CJN) Kudirat Kekere-Ekun a fadar gwamnati da ke Aso Rock.

Tinubu ya amince da nadin Kekere-Ekun bayan ritayar Olukayode Ariwoola a watan Agusta da kuma shawarar majalisar shari'a ta kasa (NJC).

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.