Sojoji Sun Gwabza da Miyagu, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda da Ceto Mutane da Dama

Sojoji Sun Gwabza da Miyagu, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda da Ceto Mutane da Dama

  • Rundunar sojin Najeriya ta gwabza kazamin fada da yan ta'adda a jihohi daban daban kuma ta samu nasarar hallaka su
  • Bayan gwabza fadan, sojojin Najeriya sun ceto mutanen da yan bindigar suka kama cikin jeji, kimanin mutum 40 sun kubuta
  • Rahotanni sun tabbatar da cewa rundunar sojin ta gwabza da yan ta'addar ne a jihohin Borno, Kaduna da wasu jihohin Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Arewa - Rundunar sojin Najeriya ta gwabza kazamar fada da yan bindiga da sauran yan ta'adda a jihohin Arewacin Najeriya.

Rahotanni sun nuna cewa sojojin sun samu nasara kan miyagun yayin da suka hallaka wasu daga cikinsu.

Sojojin Najeriya
Sojoji sun ceto mutane a hannun yan bindiga. Hoto: Kola Sulaimon
Asali: Getty Images

Jaridar Punch ta wallafa cewa rundunar sojin ta kwato makamai da dama bayan kashe yan ta'addar.

Kara karanta wannan

"Akwai matsala": Sarakuna sun roki Tinubu alfarma game da Yahaya Bello

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun gwabza da yan ta'adda a jihohi

Jaridar Leadership ta ruwaito cewa sojojin Najeriya sun yi zazzafan bincike a hanyar Lafiya zuwa Keffi inda ta kama wani da ake zargi da safarar makamai.

Haka zalika a jihar Kaduna sojoji sun fafata da yan ta'adda kamar yadda rundunar ta fatattaki miyagu a jihohin Borno da Yobe.

Dakarun Sojoji sun kwato makamai a wurare

A jihar Yobe, sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe dan ta'adda daya da kwato bindiga ƙirar AK-47 da babur.

A jihar Borno ma yan ta'addar sun tsere sun bar tulin makamai bayan sun yi musayar wuta da sojojin Najeriya.

A jihar Kaduna, sojojin sun kashe yan ta'adda da dama tare da kwato tarin makamai da suke amfani da su.

Sojoji sun ceto mutane da dama

A yayin da aka fafata tsakanin sojojin Najeriya da yan ta'adda a karamar hukumar Kukawa a jihar Borno, yan ta'adda sun gudu sun bar mutane 38 da suka sace.

Kara karanta wannan

'Zai kara aure?': Al'umma sun bayyana ra'ayoyi kan sakin Seaman Abbas

Shugaban rundunar sojin Najeriya ya yaba da ƙoƙarin sojojin inda ya ce rundunar za ta cigaba da yaki da yan ta'adda a Najeriya.

Sojoji sun yi nasara kan Boko Haram

A wani rahoton, kun ji cewa dakarun sojoji na rundunar haɗin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) sun samu nasara kan ƴan ta'addan Boko Haram a Borno.

An ruwaito cewa sojojin sun yi nasarar daƙile wani yunƙurin kai hari da ƴan ta'addan suka yi a kan titin hanyar Magumeri-Maiduguri a jihar.`

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng