Sojoji Sun Gwabza da Miyagu, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda da Ceto Mutane da Dama
- Rundunar sojin Najeriya ta gwabza kazamin fada da yan ta'adda a jihohi daban daban kuma ta samu nasarar hallaka su
- Bayan gwabza fadan, sojojin Najeriya sun ceto mutanen da yan bindigar suka kama cikin jeji, kimanin mutum 40 sun kubuta
- Rahotanni sun tabbatar da cewa rundunar sojin ta gwabza da yan ta'addar ne a jihohin Borno, Kaduna da wasu jihohin Najeriya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Arewa - Rundunar sojin Najeriya ta gwabza kazamar fada da yan bindiga da sauran yan ta'adda a jihohin Arewacin Najeriya.
Rahotanni sun nuna cewa sojojin sun samu nasara kan miyagun yayin da suka hallaka wasu daga cikinsu.

Asali: Getty Images
Jaridar Punch ta wallafa cewa rundunar sojin ta kwato makamai da dama bayan kashe yan ta'addar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sojoji sun gwabza da yan ta'adda a jihohi
Jaridar Leadership ta ruwaito cewa sojojin Najeriya sun yi zazzafan bincike a hanyar Lafiya zuwa Keffi inda ta kama wani da ake zargi da safarar makamai.
Haka zalika a jihar Kaduna sojoji sun fafata da yan ta'adda kamar yadda rundunar ta fatattaki miyagu a jihohin Borno da Yobe.
Dakarun Sojoji sun kwato makamai a wurare
A jihar Yobe, sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe dan ta'adda daya da kwato bindiga ƙirar AK-47 da babur.
A jihar Borno ma yan ta'addar sun tsere sun bar tulin makamai bayan sun yi musayar wuta da sojojin Najeriya.
A jihar Kaduna, sojojin sun kashe yan ta'adda da dama tare da kwato tarin makamai da suke amfani da su.
Sojoji sun ceto mutane da dama
A yayin da aka fafata tsakanin sojojin Najeriya da yan ta'adda a karamar hukumar Kukawa a jihar Borno, yan ta'adda sun gudu sun bar mutane 38 da suka sace.

Kara karanta wannan
Kaduna: An zargi sojoji da sake jefa bama bamai a masallaci aka kashe bayin Allah
Shugaban rundunar sojin Najeriya ya yaba da ƙoƙarin sojojin inda ya ce rundunar za ta cigaba da yaki da yan ta'adda a Najeriya.
Sojoji sun yi nasara kan Boko Haram
A wani rahoton, kun ji cewa dakarun sojoji na rundunar haɗin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) sun samu nasara kan ƴan ta'addan Boko Haram a Borno.
An ruwaito cewa sojojin sun yi nasarar daƙile wani yunƙurin kai hari da ƴan ta'addan suka yi a kan titin hanyar Magumeri-Maiduguri a jihar.`
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng