Sanusi II Ya Magantu kan Rigimar Matatar Dangote da NNPCL, Ya Gano Masu Laifi

Sanusi II Ya Magantu kan Rigimar Matatar Dangote da NNPCL, Ya Gano Masu Laifi

  • Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya yi Allah wadai da yadda ake neman kawo cikas ga matatar Aliko Dangote a Najeriya
  • Sanusi ya nuna damuwa kan yadda ake kokarin kawo cikas ga matatar da za ta jawo abubuwan cigaba ga Najeriya baki daya
  • Basaraken ya zargi wasu manya da hannu a rigimar domin cigaba da cin ribarta musamman game da farashin mai a kasar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya yi magana kan abin da ke faruwa da matatar Aliko Dangote.

Sanusi II ya ce abin takaici ne yadda aka sako matatar a gaba inda ya ce ana yin haka ne domin dakile cigaban da za ta kawo.

Kara karanta wannan

Ana shirin korar Ministoci, Ministan Tinubu ya nada hadimi, ya gargadi yan kwangila

Sanusi II ya yi magana kan rigimar matatar Dangote da NNPCL
Sarki Sanusi II ya koka kan rigimar matatar Dangote da NNPCL. Hoto: @masarautarkano, Nurphoto.
Asali: Getty Images

Sanusi II ya magantu kan matatar Dangote

Basaraken ya fadi haka ne yayin kaddamar da littafi a Abuja da tsohon Minista, Shamsudden Usman ya wallafa ta hadin guiwa, cewar Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanusi II ya zargi wasu manya a kasa jawo wannan rigima domin biyan bukatun kansu, The Guardian ta ruwaito.

Har ila yau, sarkin ya koka kan halin yan Najeriya duba da yadda suke neman kwashe dukiyar kasar ba tare da neman hanyar inganta ta ba.

Sanusi II ya koka kan halin yan Najeriya

"Kasar Najeriya ta gamu da wasu mutane da ke amfani da ita wurin cin riba madadin kawo mata cigaba."
"Wannan shi ne gaskiyar abin da ya kashe Najeriya, mutane suna shiga ofis abin da suke fara tunani shi ne nawa za su samu daga gare ta."
"Ba wai damuwarsu ta yaya za su bautawa kasar da kuma da alummarta ba wanda abin takaici ne matuka."

Kara karanta wannan

Sanatan Najeriya, Orji Uzor Kalu ya rasu? Bayanai sun fito

- Muhammadu Sanusi II

Sanusi II ya bukaci addu'a ga Dangote, BUA

A wani labarin, Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya roki ubangiji ya hada kan attajiran jihar guda biyu domin kawo mata cigaba.

Sanusi II ya kuma roki al'umma su dage da addu'o'i domin Allah ya hada kan attajiran Kano, Aliko Dangote da Abdussamad Rabiu.

Basaraken ya ce duk mai neman kawo rigima tsakanin attajiran na Kano ba son cigaban jihar ya ke yi ba ko kadan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.