Majalisar Dattawa Ta Amince da Buƙatar Tinubu, Ta Tabbatar da Naɗin CJN a Najeriya

Majalisar Dattawa Ta Amince da Buƙatar Tinubu, Ta Tabbatar da Naɗin CJN a Najeriya

  • Mai Shari'a Kudirat Kekere-Ekun ta zama sabuwar shugabar alƙalan Najeriya watau CJN bayan tantancewa a majalisar dattawa
  • Majalisar ta amince da buƙatar shugaban ƙasa Bola Tinubu, ta tabbatar da naɗin CJN a zamanta na ranar Laraba, 25 ga watan Satumba 2024
  • Tun a watan Agusta, Tinubu ya rantsar da Kudirat a matsayin muƙaddashin CJN bayan Mai Shari'a Ariwoola ya yi ritaya daga aiki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun a matsayin alkalin alkalan Najeriya (CJN).

Tun a watan Agusta, Kudirat Kekere-Ekun ta zama muƙaddashin CJN bayan Mai Shari'a Olukayode Ariwoola ya yi ritaya daga aiki.

Kudirat Kekere-Ekun da Bola Tinubu.
Majalisar dattawa ta amince da naɗin sabuwar alƙalin alƙalai CJN a Najeriya Hoto: @OfficialABAT
Asali: Twitter

Daily Trust ta ce CJN ta samu rakiyar wasu alkalan kotun koli da na kotun daukaka kara zuwa zauren majalisar dattijai da karfe 12:30 na tsakar rana yau Laraba.

Kara karanta wannan

Majalisar Dattawa ta fara tantance sabuwar shugabar alƙalan Najeriya, an samu bayanai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bola Tinubu ya aika saƙo majalisar dattawa

Wannan na zuwa ne bayan shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya buƙaci majalisar dattawan ta tabbatar da naɗinta a wata wasika da ya aika jiya Talata.

Bayan karanta wasiƙar, shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya miƙa bukatar ga kwamitin da ya kunshi dukkan sanatoci domin tantancewa ranar Laraba.

Bayan kammala tattaunawa da tantancewa, Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Kudirat Kekere-Ekun a matsayin sabuwar CJN a Najeriya.

Sabuwar CJN ta sha alwashin kawo sauyi

A yayin tantancewa a zauren majalisa, Mai shari’a Kekere-Ekun ta ce za ta yi amfani da fasahar zamani don tabbatar an yi wa mutane adalci cikin ƙankanin lokaci.

Haka nan kuma ta bayyana cewa mssu cin hanci da rashawa masu aikata miyagun laifuka sun shiga uku a hannun shari'a domin ba za su da wurin ɓuya.

Kara karanta wannan

Tinubu ya kunyata majalisar tarayya, ya ki rattaba hannu kan kudurin da aka kawo

Sabuwar CJN ta sha alwashin yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da ɓangaren shari'a ya dogara da kansa, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Rasuwar sanata ta hana zaman majalisa

Kun ji cewa Majalisar wakilai ta ɗage zamanta na farko bayan dawowa daga hutun shekara-shekara domin jimami da karrama marigayi Sanata Ifeanyi Ubah.

Sanatan mai wakiltar Anambra ta Kudu a majalksar dattawa ya riga mu gidan gaskiya ne a watan Yuli lokacin ƴan majalisa sun tafi hutu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262