“Ka Cire Tallafi Gaba Daya”: Dangote Ya Shawarci Tinubu Ana Tsaka da Korafi

“Ka Cire Tallafi Gaba Daya”: Dangote Ya Shawarci Tinubu Ana Tsaka da Korafi

  • Attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote ya yi magana kan cire tallafin man fetur inda ya ba Shugaba Bola Tinubu shawara
  • Dangote ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta cire maganar biyan tallafin man fetur gaba daya domin daidaita lamura
  • Hakan ya biyo bayan korafe-korafe da ake ta yi bayan cire tallafin man fetur da ya jefa al'umma cikin mawuyacin hali

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shahararren dan kasuwa, Alhaji Aliko Dangote ya shawarci Bola Tinubu kan cire tallafin man fetur.

Dangote ya ce wannan shi ne lokacin da ya dace Tinubu ya cire tallafin gaba daya domin daidaita lamura.

Dangote ya yi magana game da cire tallafin mai
Aliko Dangote ya bukaci Tinubu ya cire tallafin mai gaba daya. Hoto: Dangote Industries.
Asali: Getty Images

Dangote ya yi magana kan cire tallafi

Kara karanta wannan

Rundunar tsaro ta fadi halin da Turji ke ciki bayan kisan Sabubu, ta sha alwashi

Attajirin ya bayyana haka ne yayin hira da gidan talabjin na Bloomberg a jiya Litinin 23 ga watan Satumbar 2024 da Punch ta bibiya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dangote ya ce maganar cire tallafin mai abu ne mai sarkakkiya inda ya ce da za ran gwamnati ta cire tallafi, mutane za su kara farashi.

Ya ce hakan zai tilasta gwamnati biyan kudin da bai kamata tana cigaba da biya ba.

"Ina tunanin wannan shi ne lokacin da ya dace a rabu da maganar tallafi saboda duka kasashe sun tsayar da ba da tallafi."

- Aliko Dangote

"Gwamnati ba za ta iya biya ba" - Dangote

Dangote ya ce cigaba da biyan tallafin mai ba zai dore ba inda ya ce gwamnati ba za ta iya cigaba da biya ba, kamar yadda TheCable ta ruwaito.

Ya kara da cewa wannan ya ragewa gwamnati ta duba ko ta cigaba da biyan tallafin ko kuma ta dakatar da shi.

Kara karanta wannan

Tsohon shugaban NESG ya faɗi kuskuren Tinubu da ya jefa ƴan Najeriya cikin wahala

Dillalan mai sun guji matatar Dangote

Kun ji cewa matatar man Dangote ta koka kan yadda dillalan mai da suka yanke shawarar cigaba da shigo da mai daga ketare.

Matatar da zargi dillalan da shigo da fetur da ba shi da kyau da kuma inganci da zai kawo nakasu a harkar mai.

Wannan na zuwa ne bayan manyan dillalan mai guda uku a Najeriya sun dauki matakin dauko man daga kasashen waje.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.