Seaman Abbas: DHQ Ta Yi Magana kan Zargin Tsare Sojan Ruwa na Shekara 6

Seaman Abbas: DHQ Ta Yi Magana kan Zargin Tsare Sojan Ruwa na Shekara 6

  • Hedkwatar tsaro ta ƙasa ta yi martani kan zargin cewa an tsare wani sojan ruwa har na tsawon shekara shida bisa rashin adalci
  • Daraktan yaɗa labarai na DHQ ya bayyana cewa ba a taɓa kama Seaman Abbas ba kamar yadda matarsa ta yi zargi
  • Ya yi bayanin cewa za a gayawa ƴan Najeriya komai kan lamarin da zarar an kammala binciken da ake gudanarwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Hedkwatar tsaro ta ƙasa (DHQ) ta ce Seaman Abbas Haruna, wanda ake zargin an tsare shi tsawon shekara shida, ba a taɓa kama shi ba.

Matar Abbas Haruna, Hussaina Iliya, ta je wani gidan rediyo mai farin jini a Abuja inda ta zargi sojoji da tsare mijinta bisa rashin adalci tun shekarar 2018.

Kara karanta wannan

Karkatar da tallafi: Ɗan majalisa ya fusata, ya shirya maka gwamna a gaban kotu

DHQ ta musanta tsare Seaman Abbas
DHQ ta ce ba a taba kama Seaman Abbas ba Hoto: @HQNigerianArmy
Asali: Facebook

Hakan ya sanya babban hafsan tsaron ƙasa, Janar Christopher Musa, da ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle, suka bayar da umarnin gudanar da bincike kan lamarin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me DHQ ta ce kan tsare Seaman Abbas?

A wata hira da wakilin jaridar The Punch a ranar Asabar, daraktan yaɗa labarai na DHQ, Birgediya Janar Tukur Gusau, ya ce ba a taɓa kama Abbas Haruna ba.

"Ba a taɓa kama shi ba. Mutane kawai suna yin surutu ne kan abin da ba haka yake ba."

- Birgediya Janar Tukur Gusau

Da aka tambaye shi inda yake tun lokacin da matarsa ​​ta yi iƙirarin cewa ya shafe shekara shida a hannun sojoji, Tukur Gusau ya ce za a bayyana hakan bayan an kammala bincike.

"A halin yanzu ana ci gaba da bincike. A lokacin da rahoton binciken ya kammala, za mu sanar da ƴan Najeriya abin da ya faru da kuma inda yake."

Kara karanta wannan

Kumallon mata: Wata matar aure a Kano ta zuba 'fiya fiya' a abincin ɗan kishiyarta

- Birgediya Janar Tukur Gusau

DHQ ta musanta zargin matar Abbas

Da aka ƙara matsa masa lamba kan maganar matar, Tukur Gusau ya ce matar Abbas Haruna ta san ba a kama mijinta ba.

"Ta san ba a kama mijinta ba. A lokacin da ya dace, za mu sanar da mutane abin da ya faru."

- Birgediya Janar Tukur Gusau

NEF ta yi Allah wadai kan tsare Seaman Abbas

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar Northern Elders Forum (NEF) ta bayyana damuwa kan halin da jami'in rundunar sojin ruwa na kasa, Seaman Abbas Haruna ke ciki.

A martanin da ta yi, ƙungiyar NEF ta ce akwai damuwa da alamomin tambaya kan yadda ake bautar da jami'an da ke kokarin kare martabar ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng