Seaman Abbas: DHQ Ta Yi Magana kan Zargin Tsare Sojan Ruwa na Shekara 6
- Hedkwatar tsaro ta ƙasa ta yi martani kan zargin cewa an tsare wani sojan ruwa har na tsawon shekara shida bisa rashin adalci
- Daraktan yaɗa labarai na DHQ ya bayyana cewa ba a taɓa kama Seaman Abbas ba kamar yadda matarsa ta yi zargi
- Ya yi bayanin cewa za a gayawa ƴan Najeriya komai kan lamarin da zarar an kammala binciken da ake gudanarwa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Hedkwatar tsaro ta ƙasa (DHQ) ta ce Seaman Abbas Haruna, wanda ake zargin an tsare shi tsawon shekara shida, ba a taɓa kama shi ba.
Matar Abbas Haruna, Hussaina Iliya, ta je wani gidan rediyo mai farin jini a Abuja inda ta zargi sojoji da tsare mijinta bisa rashin adalci tun shekarar 2018.

Source: Facebook
Hakan ya sanya babban hafsan tsaron ƙasa, Janar Christopher Musa, da ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle, suka bayar da umarnin gudanar da bincike kan lamarin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Me DHQ ta ce kan tsare Seaman Abbas?
A wata hira da wakilin jaridar The Punch a ranar Asabar, daraktan yaɗa labarai na DHQ, Birgediya Janar Tukur Gusau, ya ce ba a taɓa kama Abbas Haruna ba.
"Ba a taɓa kama shi ba. Mutane kawai suna yin surutu ne kan abin da ba haka yake ba."
- Birgediya Janar Tukur Gusau
Da aka tambaye shi inda yake tun lokacin da matarsa ta yi iƙirarin cewa ya shafe shekara shida a hannun sojoji, Tukur Gusau ya ce za a bayyana hakan bayan an kammala bincike.
"A halin yanzu ana ci gaba da bincike. A lokacin da rahoton binciken ya kammala, za mu sanar da ƴan Najeriya abin da ya faru da kuma inda yake."

Kara karanta wannan
Kumallon mata: Wata matar aure a Kano ta zuba 'fiya fiya' a abincin ɗan kishiyarta
- Birgediya Janar Tukur Gusau
DHQ ta musanta zargin matar Abbas
Da aka ƙara matsa masa lamba kan maganar matar, Tukur Gusau ya ce matar Abbas Haruna ta san ba a kama mijinta ba.
"Ta san ba a kama mijinta ba. A lokacin da ya dace, za mu sanar da mutane abin da ya faru."
- Birgediya Janar Tukur Gusau
NEF ta yi Allah wadai kan tsare Seaman Abbas
A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar Northern Elders Forum (NEF) ta bayyana damuwa kan halin da jami'in rundunar sojin ruwa na kasa, Seaman Abbas Haruna ke ciki.
A martanin da ta yi, ƙungiyar NEF ta ce akwai damuwa da alamomin tambaya kan yadda ake bautar da jami'an da ke kokarin kare martabar ƙasar nan.
Asali: Legit.ng
