Abubuwa 7 da Tinubu Ya Iske a Ofis da Suka Hana Zuwa Taron Majalisar Dinkin Duniya

Abubuwa 7 da Tinubu Ya Iske a Ofis da Suka Hana Zuwa Taron Majalisar Dinkin Duniya

Abuja - A makon nan Mai girma Bola Ahmed Tinubu ya dawo Najeriya bayan ya shafe kwanaki masu yawa a kasashen ketare.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Mai girma Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci kasar Sin, Hadaddiyar daular Larabawa da Birtaniya kafin ya dawo a makon nan.

Bola Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya hakura da zuwa taron Majalisar Dinkin Duniya a Amurka Hoto: @Dolusegun
Asali: Twitter

Bola Tinubu ba zai je taron MDD ba

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yarda cewa akwai ayyuka da yawa a gabansa, saboda haka ne ya fasa komawa taro a Amurka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kashim Shettima ne zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron majalisar dinkin duniya yayin da Tinubu ke fama da rikicin gida.

Rahoton nan ya tattaro abubuwan da za su ba shugaba Tinubu ciwon-kai daga dawowarsa don haka za a bukaci shawo kansu.

Kara karanta wannan

"Ba maganar kwasar kudi ba ne": Tinubu ya fadi dalilin zuwansa 'Aso Rock'

1. Ambaliyar Maiduguri

Shigowarsa Najeriya yake da wuya sai aka ji Bola Tinubu ya isa jihar Borno domin jajantawa al’umma kan ambaliyar da aka yi kwanaki.

Shugaban kasar ya dauki wasu matakai dabam-dabam kuma ana sa ran gwamnatinsa ta magance aukuwar matsalar a sauran jihohi.

2. Karin kudin fetur

A duk fadin Najeriya yanzu ana kuka game da karin farashin man fetur da aka yi inda aka ji cewa lita ta doshi N1, 000 a wasu garuruwan.

An samu karin ne lokacin da aka fara tace mai a gida saboda haka dole shugaban kasa ya kawo karshen sabanin kamfanin Dangote da NNPCL.

3. ‘Yan bindiga a jihohin Arewa

Dama can mai girma shugaban kasa ya bukaci a ga bayan ‘yan bindigan da suka addabi musamman jihohin da ke Arewa maso yamma.

An yi nasarar hallaka Halilu Buzu da wasu miyagun, shugaban kasan yana sa rai sojoji su ga bayan irinsu Bello Turji da ake nema ido rufe.

Kara karanta wannan

Tinubu ya fasa halartar taron Majalisar Dinkin Duniya, an fadi dalilin zama a gida

4. Barazanar ‘yan kwadago

‘Yan kwadago da ‘yan fansho sun fara nuna cewa tun da kudin fetur ya tashi, ba za ta yiwu N70, 000 ya zama mafi karancin albashi ba.

Shugaban NLC, Kwamred Joe Ajaero ya nuna za a koma teburin zama da gwamnatin tarayya a sakamakon tashin farashin man fetur.

5. ASUU da ma’aikatan jami’o’i

Bayan kungiyoyin NLC da NUP, shugaba Tinubu zai yi fama da ma’aikatan jami’o’i; NASU da SSANU da ke barazanar yajin aiki a kasar.

Kafin tafiyarsa Sin, UAE da Birtaniya, gwamnatinsa ta na kokarin tattaunawa da shugabannin ASUU domin hana ta rufe jami’o’i.

6. Zaben gwamnan Edo

Yanzu kowa dai ya zura ido domin ganin yadda hukumar INEC za ta gudanar da zaben sabon gwamnan jihar Edo a karshen makon nan.

Jam’iyyar shugaban kasar watau APC ta dage sai ta karbe jihar daga hannun Godwin Obaseki da PDP da ke zargi jami’an tsaro da son-kai.

Kara karanta wannan

Tinubu na shirin rusa wata ma'aikata, an matsa masa lamba ya kori wasu ministoci

7. Canji a gwamnatin tarayya

Bayan dawowar shugaban kasa aka ji ya gana da Farfesa Attahiru Jega wanda ya gabatar da rahoton kafa ma'aikatar raya kiwon dabbobi.

Ana rade-radin za a yi sauyi a gwamnatin tarayya kuma watakila shugaban kasar ya rusa wasu ma'aikatu idan ya tashi sauya ministoci.

Sojoji sun kashe Halilu Buzu

‘Dan ta’ddan nan Halilu Sabubu Buzu wanda aka ce uban gidan Bello Turji ne ya tafi inda kowa zai je kamar yadda rahoto ya bayyana a baya.

A wani kauye dakarun Operation Hadarin Daji suka yi wa ‘yan bindigan kwantan bauna. Bayan bindige Buzu, ana neman Bello Turji yanzu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng