EFCC Ta Fadi yadda Ta yi Gumurzu kan Yunkurin Kama Yahaya Bello

EFCC Ta Fadi yadda Ta yi Gumurzu kan Yunkurin Kama Yahaya Bello

  • Hukuma mai yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta yi karin haske kan yunkurin kama Yahaya Bello da jami'anta suka yi
  • Hukumar EFCC ta zargi gwamnan jihar Kogi, Usman Ododo da boye Yahaya Bello yayin da jami'anta suka yi yunkurin cafke shi
  • EFCC na zargin tsohon gwamnan jihar Kogi ne kan karkatar da makudan kudi har Naira biliyan 80.2 kuma tana nemansa ido rufe

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Hukuma mai yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta magantu kan yunkurin kama Yahaya Bello.

EFCC ta bayyana cewa ta samu katsalandan daga gwamnan jihar Kogi na yanzu wajen ba Yahaya Bello kariya.

Kara karanta wannan

EFCC vs Yahaya Bello: Tsohon gwamna ya sake tserewa hukuma kan zargin rashawa

Yahaya Bello
EFCC ta fadi yadda Yahaya Bello ya kubuce mata. Hoto: Yahaya Bello|EFCC
Asali: Facebook

Jaridar Punch ta wallafa cewa kakakin hukumar EFCC, Dele Oyewale ne ya bayyana yadda abin ya faru.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda aka so cafke Yahaya Bello

A ranar Laraba aka ji karan harbe harbe a wani gida yayin da jami'an hukumar EFCC suka yi yunkurin kama Yahaya Bello.

Hakan ya biyo bayan ikirarin da tsohon gwamnan jihar Kogin ya yi ne kan cewa ya mika wuya ga gayyatar da EFCC ta masa.

Haka dai jami'an EFCC suka gama kai ruwa rana gidan da suke zargi Yahaya Bello na ciki ba tare da sun samu kama shi ba.

Ododo ya taimaki Yahaya Bello inji EFCC

Hukumar EFCC ta ce abin da ya hana ta cafke Yahaya Bello shi ne kariyar da ya samu daga gwamna Usman Ahmed Ododo.

Legit ta ruwato cewa EFCC ta ce Usman Ahmed Ododo yana amfani da rigar kariya da yake da ita wajen boye Yahaya Bello daga kamu.

Kara karanta wannan

An yi watsi da albashin N70,000, an bukaci NLC ta tursasawa Tinubu biyan N250,000

Manema labarai sun yi yunkurin ji ta bakin jami'an yada labaran Yahaya Bello amma ba su ba da amsa ba har a lokacin hada rahoton.

PDP ta bukaci a binciki Ahmed Aliyu

A wani rahoton, kun ji cewa yayin da ake surutu kan gyaran bohula a jihar Sokoto, jam'iyyar PDP ta bukaci binciken Gwamna Ahmed Aliyu.

Rahotanni sun nuna cewa jam'iyyar PDP ta yi Allah wadai da sake ware makudan kudi har N30bn domin katange hanyoyi a jihar Sokoto.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng