"An Karya Doka," An Taso NNPC a Gaba kan Farashin Man Fetur na Matatar Ɗangote

"An Karya Doka," An Taso NNPC a Gaba kan Farashin Man Fetur na Matatar Ɗangote

  • Babban lauya a Najeriya kuma mai fafutukar kare hakkin ɗan adam, Femi Falana SAN ya caccaki kamfanin NNPCL
  • Falana SAN ya ce ƙayyade farashin man da kamfanin NNPC ya yi ya saɓawa sashi na 205 na dokar man fetur PIA
  • Wannan na zuwa ne bayan kamfanin mai ya fara jigilar fetur daga matatar Ɗangote ranar Lahadin da ta gabata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Fitaccen lauyan nan ɗan fafutukar kare haƙƙin ɗan adam, Femi Falana (SAN), ya yi magana kan farashin man feturin matatar Ɗangote.

Falana ya bayyana cewa a tsarin doka, haramun ne kamfanin mai na kasa NNPCL ya tsoma baki ko ya tsaida farashin man fetur da matatar Ɗangote ta tace.

Kara karanta wannan

Ana murnar kisan ubangidan Bello Turji, gwamna ya ƙara tona badaƙalar ministan Tinubu

Femi Falana SAN.
Femi Falana ya ce NNPCL ya take doka da ya yanke farashin.maɓ fetur na matatar Ɗangote Hoto: Femi Falana
Asali: Twitter

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Femi Falana ya fitar ranar Talata, 17 ga watan Satumba, 2024, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NNPCL ya saɓawa tanadin dokar PIA

Bisa haka Falana ya ce yanke farashin man Ɗangote da NNPCL ya yi ya saɓawa tanadin sashi na 205 na dokar man fetur PIA.

Lauyan ya ce:

"Ranar 5 ga watan Satumba, NNPC ya fito ya sanar da cewa matsalar canjin kuɗin waje ne ya kawo tashin farashin man fetur kamar yadda dokar PIA ta tanada.
"Mataimakin shugaban sashen harkokin mai na NNPC, Mr. Adedapo Segun da kansa ya ce sashe na 205 a PIA ya tanadi cewa yanayin kasuwa ne ke ƙayyade farashin mai.
"A cewarsa, an maida komai hannun ƴan kasuwa ma'ana babu ruwan gwamnati ko kamfanin NNPC wajen yanke farashin litar fetur."

Kara karanta wannan

NMA ta hango wata matsala bayan ambaliya a Maiduguri, ta ba da mafita

Falana ya faɗi dokar da NNPCL ya karya

Femi Falana ya ƙara da cewa NNPCL ya yi tufka da warwara, ya fito ya sanar da farashin da za a sayar da man feturin matatar Ɗangote.

Ya ce abin da NNPCL ya yi na ƙayyaɗe farashin ya saɓawa sashi na 205 na dokar PIA, wanda ya ce a bar yanayin kasuwa ya ƙayyade farashin litar man fetur.

Kalaman babban lauyan na zuwa ne bayan kamfanin mai ya fara jigilar fetur daga matatar Ɗangote ranar Lahadi a cewar rahoton Daily Post.

Yan kasuwa na shirin tsallake matatar Ɗangote

A wani rahoton kuma dillalan mai sun bayyana cewa fetur din da matatar Dangote ta tace ya yi matukar tsada a kasuwa.

Wannan ta sa yan kasuwar su ka fara tunanin fara sayo man fetur da kudinsu kai tsaye daga kasashen wajen zuwa kasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262