'Yan Bindiga Sun Tashi Bama Bamai a Ofishin Ƴan Sanda, An Rasa Rayuka

'Yan Bindiga Sun Tashi Bama Bamai a Ofishin Ƴan Sanda, An Rasa Rayuka

  • Ƴan bindiga sun kai hari tare da tashin bama-bamai a wani caji ofis na ƙaramar hukumar Orumba ta Kudu a jihar Anambra
  • Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa maharan sun kashe ƴan sanda uku, wasu da dama sun samu raunuka
  • Kakakin ƴan sandan Anambra, Tochukwu Ikenga ya ce jami'an tsaro sun kwance bama-bamai biyar a wurin bayan tafiyar maharan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Anambra - Wasu ƴan bindiga da ake kyautata zaton mayaƙan kungiyar IPOB ne sun kai mummunan hari caji ofis na ƴan sanda a jihar Anambra.

Bayanai sun nuna cewa ƴan ta'addan sun hallaka jami'an ƴan sanda uku a harin wanda suka yi amfani da bama-bamai yau Litinin, 16 ga watan Satumba, 2024.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun hallaka shugaban babbar kasuwa a cikin dare

Sufetan yan sanda, IGP Kayode.
Jami'ai 3 sun mutu da wasu yan bindiga suka kai farmaki caji ofis a Anambra Hoto: @PoliceNG
Asali: Facebook

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na safiyar ranar Litinin a karamar hukumar Orumba ta Kudu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jami'an tsaro sun gano ƙarin bama-bamai

Bayan harin, jami’an tsaron hadin gwiwa da suka hada da sojoji, ƴan Sanda, jami'an NSCDC da ‘yan banga sun gano wasu bama-bamai guda biyar da ba su kai ga tashi ba a wurin. 

Rahotanni sun nuna cewa ƴan bindigar na yunkurin tabbatar da bin dokar zaman gida ta ranar Litinin a lokacin da suka yi arangama da jami'an tsaro.

Ganau sun shaida cewa aƙalla ƴan sanda uku ne suka rasa rayukansu a harin, wasu kuma sun samu raunuka.

An kashe ƴan sanda a bakin aiki

A ruwayar Daily Trust, jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan jihar Anambra, Tochukwu Ikenga ya tabbatar da cewa jami'an ƴan sanda biyu aka kashe a harin.

Kara karanta wannan

Wani Jirgi ya gamu da haɗari a Najeriya, an nemi wasu fasinjoji an rasa

"Maharan waɗanda ake zargin ƴan haramtacciyar ƙungiyar ƴan aware ne sun kutsa kai caji ofis ɗauke da bama-bamai, suka buɗe wuta kan mai uwa ɗa wani, wuta ta kama."
"Abin takaici ƴan sanda biyu da suka yi kokarin ɗaƙile harin sun rasa rayukansu, tuni aka ajiye gawarwakinsu a ɗakin ajiyar gawa," in ji Ikenga.

Ƴan bindiga sun shiga sakatariyar ƙaramar hukuma

A wani rahoton kuma wasu yan bindiga kimanin 30 sun dura ƙaramar hukumar Ogbaru a jihar Anambra inda suka bude wuta a sakatariya.

Rahotanni sun nuna cewa yan bindigar sun yi kone kone a karamar hukumar kafin su yi musayar wuta da yan sandan jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262