Bichi: Ɗan Tsohon Daraktan DSS Ya Yi Martani kan Zargin Sace $2m na Mahaifinsa

Bichi: Ɗan Tsohon Daraktan DSS Ya Yi Martani kan Zargin Sace $2m na Mahaifinsa

  • Yayin da ake ta yada cewa Abba Bichi ya tsere da kudin mahaifinsa, matashin ya yi martani kan rade-radin da ake yi
  • Abba wanda ɗa ne ga tsohon daraktan DSS, Yusuf Magaji Bichi ya ƙaryata jita-jitar inda ya ce ana son bata musu suna ne
  • Wannan na zuwa ne bayan rade-radin cewa Abba ya sace kudin mahaifinsa har $2m inda ake zargin ya tsere da su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Dan tsohon daraktan DSS, Yusuf Magaji Bichi ya yi martani kan rade-radin da ake yi a kansa

Abba Bichi ya musanta labarin cewa ya tsere bayan sace $2m na mahaifinsa da ake ta yadawa a kafofin sadarwa.

Kara karanta wannan

Bayan shekaru, Gwamna Abba ya sakawa yarinyar da taimaka masa a zaben 2019

Abba Bichi ya mayar da martani kan zargin satar $2m da ake masa
Dan tsohon daraktan DSS, Yusuf Magaji Bichi ya musanta zargin satar $2m na mahaifinsa. Hoto: @Uchechukwubiaf4.
Asali: Twitter

Abba Bichi ya ƙaryata jita-jitar satar $2m

Matashin dan kwallon ya ce babu kamshin gaskiya a labarin inda ya ce an yi ne domin bata musu suna, cewar rahoton The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abba ya yi martanin ne yayin da ya ke cikin wani filin wasa a kasar Jamus inda ya ce ya mayar da hankalinsa kan wasan kwallon kafa.

"Ba gudu na ke yi ba, ina faman gina rayuwa ta ne a matsayin dan kwallo, jita-jitar da ake yadawa karairayi ne kuma abin dariya."

- Abba Bichi

Yusuf Bichi ya yi fatali da rade-radin

Har ila yau, Yusuf Bichi shi ma ya yi magana kan lamarin inda ya yi fatali da rade-radin da ake yadawa.

Yusuf Bichi ya nuna goyon baya ga dan nasa musamman bayan ƙungiyarsa ta yi rashin nasara a wasan da ta buga, cewar rahoton Pulse.

Kara karanta wannan

Dan takarar shugaban kasa na neman muƙamin mataimaki a 2027? ya yi magana

DSS ta cafke lakcara a Jami'ar Abuja

Kun ji cewa ana zargin jami'an hukumar DSS a Najeriya sun kama wani lakcara a Jami'ar Baze da ke birnin Abuja, Dr. Abubakar Alkali.

An wuce da Alkali ne zuwa jihar Sokoto fiye da makwanni uku kan zargin goyon bayan zanga-zanga da aka yi a Najeriya.

Wannan na zuwa ne bayan gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.