Ambaliya: Gwamnatin Tarayya, Dangote, Dantata da Wadanda Su ka ba Borno Tallafi

Ambaliya: Gwamnatin Tarayya, Dangote, Dantata da Wadanda Su ka ba Borno Tallafi

  • Gwamnatin tarayya ta ba da Naira biliyan uku ga jihar Borno a sakamakon ambaliyar ruwan da ta barke
  • Mai kudin Najeriya da Afrika ya ba hukumar NEMA tallafin N1.5bn ta hannunsa da kuma gidauniyar Aliko Dangote
  • Gwamnonin jihohi da ‘yan majalisar tarayya sun aiko da gudumuwa kuma ana sa ran wasu za su cigaba da aikowa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Borno - A sakamakon ambaliyar ruwan da ta rutsa da Maiduguri a jihar Borno, ana cigaba da taimakawa gwamnati da tallafi.

Rahoton nan ya yi kokarin tattaro attajirai, gwamnatoci da ‘yan siyasar da suka ba da gudumuwa domin taimakawa jihar Borno.

Ambaliya a Borno
Ana taimakawa al'umma bayan samun ambaliyar ruwa a Borno Hoto: @Yadomah
Asali: Twitter

Tallafin ambaliya a jihar Borno

1. Gwamnatin tarayya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Ambaliya: Dattijon attajiri, Dantata ya tallafa wa Borno da sama da Naira biliyan 1

Lamarin ya na faruwa sai aka ji gwamnatin tarayya ta aikowa jihar Borno N3bn domin magance matsalar da jama’a suka shiga.

Tribune ta rahoto gwamna Babagana Zulum ya na wannan bayani lokacin da ya ziyarci wani sansanin da aka yi wa ‘yan gudun hijira.

2. Aliko Dangote

Mai kudin Afrika, Aliko Dangote ya ce hukumar NEMA ta nemi ya kawo tallafi, saboda haka aka amince a ba da gudumuwar N1bn.

Bayan nan kuma gidauniyar ‘dan kasuwan ta kara da N500m kamar yadda labarin ya zo a jaridar The Cable a yammacin ranar Juma’a.

3. Jihar Adamawa

A madadin gwamnatin Adamawa, mai girma Ahmadu Umar Fintiri ya ba da gudumuwar N50m a matsayin gudumuwar ambaliya.

Baya ga kudi, an rahoto cewa gwamnan jihar Adamawa ya ba jihar kyautar jiragen ruwa.

4. Jihar Gombe

Gwamnati da mutanen Gombe sun ba da gudumuwar kudi har N100m domin a taimaki bayin Allah da ambaliya ta shafa a Maiduguri.

Kara karanta wannan

'Ka da mu zargi kowa': Tinubu ya bayyana abin da ya jawo ambaliyar Maiduguri

Jaridar Punch ta ce mataimakin gwamnan jihar Gombe ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi wa mutanen Borno Allah kyauta.

5. Jihar Nasarawa

Rahoto ya gabata cewa gwamna Abdullahi Sule ya sanar da cewa ya aiko da motocin kayan abinci domin a taimakawa gwamnatin Borno.

Mai girma gwamnan Nasarawa bai fadi adadin motocin abincin da ya aikowa jama’a ba.

6. Hon. Mukhtar Betara

Baya an ji cewa ‘dan majalisar wakilan tarayya, Mukhtar Betara ya taimaka da gudumuwar N10m bayan jin labarin wannan ambaliyar.

Hon. Betara mai wakiltar mutanen Biu/Bayo/Shani and Kwaya Kusar yana sa ran kudin zai rage radadin da mutanen jiharsa suka shiga.

7. Atiku Abubakar

Daily Trust ta ce tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ba gwamnatin Borno gudumuwar N100m a ranar Lahadi.

8. Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano ta ba da tallafin N100m a sanadiyyar ambaliyar. Wasu kwamishononin Abba Kabir Yusuf suka sanar da haka.

9. Aminu Dantata

Kara karanta wannan

NMA ta hango wata matsala bayan ambaliya a Maiduguri, ta ba da mafita

A ranar Talata aka samu labari cewa Alhaji Aminu Dantata, ya ba da tallafin Naira biliyan 1.5 ga mutanen da ambaliya ta shafa a Borno.

An fara samun saukin ambaliyar Borno

A baya an samu labari ruwan da mamaye Maiduguri ya fara janyewa bayan mutane sun yi kwana da kwanaki a yanayi mai ban tausayi.

Jami'an hukumar SEMA da sauran jama'a na bada agajin gaggawa kuma zuwa yammacin Alhamis, mutane 3,682 aka ceto a Borno.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng