DSS Ta Tsorata, Ta Saki Ajaero Mintuna Kafin Wa’adin Kungiyar NLC Ya Cika

DSS Ta Tsorata, Ta Saki Ajaero Mintuna Kafin Wa’adin Kungiyar NLC Ya Cika

  • KuMintuna kafin wa'adin da kungiyar NLC ta ba gwamnatin Bola Tinubu ya cika, hukumar DSS ta saki Kwamred Joe Ajaero
  • Kungiyar NLC da TUC sun yi barazanar dakatar da komai a kasar wanda suke ganin zai taba tattalin arziki idan ba a sake shi ba
  • Hakan ya biyo bayan cafke Ajaero da DSS ta yi a birnin Abuja yana shirin zuwa Landan domin babban taron kungiyar kwadago

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Hukumar DSS ta sako shugaban kungiyar kwadago, NLC, Kwamred Joe Ajaero da tsakar dare.

Hukumar ta sake shugaban kungiyar ne mintuna kafin wa'adin da NLC ta ba gwamnatin Bola Tinubu ya cika.

Kara karanta wannan

NLC ta na son jiƙawa Tinubu aiki, ta bukaci rage kudin fetur a jerin bukatu 4

DSS ta sako shugaban kungiyar NLC bayan yi wa gwamnatin Tinubu barazana
Hukumar DSS ta sake shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero. Hoto: @NLCHeadquarters, @OfficialDSSNG.
Asali: Facebook

DSS ta sake shugaban NLC, Joe Ajaero

Daily Trust ta ce an kama Ajaero ne a jiya Litinin 9 ga watan Satumbar 2024 a filin tashi da saukar jiragen saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ajaero ya shirya tafiya Burtaniya ne domin halartar wani taro da kungiyar 'yan kasuwar kasar a birnin Landan.

Wani babban ma'aikacin NLC ya tabbatar da sako Ajaero inda ya ce an sake shi ne bisa sharadin beli da aka bayar.

Barazanar da NLC ta yi wa gwamnati

Bayan kama Ajaero ne kungiyoyin NLC da TUC suka yi barazanar dakatar da komai a kasar wanda hakan ka iya shafar tattalin arzikin Najeriya.

Hakan ya biyo bayan shirin NLC domin fara zanga-zanga a kasar idan har gwamnati ba ta sake Ajaero zuwa karfe 12.00 na dare.

Lauyan Ajaero, Maxwell Opara ya ce DSS sun cafke Ajaero duk da sanar da su da ya yi na tafiya zuwa Burtaniya, cewar rahoton Premium Times.

Kara karanta wannan

Bayanai sun fito kan dalilin kama shugaban kwadago da DSS ta yi

An fadi dalilin kama Ajaero a Abuja

Kun ji cewa rahotanni da suka fito daga wasu jami'an tsaro sun nuna an kama shugaban kwadago ne bisa zargin kin amsa gayyatar 'yan sanda.

Ana hasashen cewa wani kamfanin jigilar jiragen sama ne ya kai Joe Ajaero kara wajen 'yan sandan Najeriya kan wasu abubuwa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.