'Abin da Ya Sa Dangote ba Zai Siyar da Mai Kasa da Farashin Kamfanin NNPCL ba'

'Abin da Ya Sa Dangote ba Zai Siyar da Mai Kasa da Farashin Kamfanin NNPCL ba'

  • Wani masanin harkokin mai a Najeriya, Henry Adigun ya yi fashin baki kan farashin da matatar Dangote za ta tsaida
  • Adigun ya ce ba zai taba yiwuwa Dangote ya siyar a farashi kasa da na kamfanin NNPCL ba saboda ana lissafi da dala ne
  • Mai fashin bakin ya kuma ce man Dangote shi ne mafi kyau a duniya domin haka duk abin da yake da kyau zai yi tsada

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Wani masanin harkokin man fetur a Najeriya ya yi magana kan farashin mai a matatar Aliko Dangote.

Mr. Henry Adigun ya ce zai yi wahala Dangote ya siyar da mai kasa da farashin kamfanin NNPCL a yanzu.

Kara karanta wannan

Dangote: NNPC ya ba matatun Najeriya ikon sayar da fetur kai tsaye ga 'yan kasuwa

Masanin harkokin mai ya yi magana kan farashin fetur a matatar Dangote
Masanin a harkokin mai, Henry Adigun ya ce da wahala Dangote ya siyar da mai da araha. Hoto: Bloomberg/Contributor.
Asali: UGC

Masani ya magantu kan farashin man Dangote

Adigun ya bayyana haka ne a yau Juma'a 6 ga watan Satumbar 2024 yayin hira da Channels TV.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Masanin ya ce yawan amfani da dala a harkokin gudanar da matatar shi ne babban dalilin da ya sa man zai yi tsada.

Ya ce man da matatar Dangote ke fitarwa shi ne mafi kyau a duniya wanda dole zai saka ya yi tsada.

'Man Dangote shi ne mafi kyau' - Masani

"Ina cigaba da fadawa mutane, Dangote ya dauki bashi a dala ba Naira ba, kuma zai cigaba da biyan bashin a dala."
"Ba zai taba siyarwa kasa da N850 na NNPCL ba kamar yadda ake zato saboda akwai kudi da ake kashewa na shiga da wani kaso na mai."

- Henry Adigun

Adigun ya ce Dangote yana samun 40% ne na danyen mai daga NNPCL sannan ya siyo sauran daga Amurka saboda ba za a yi amfani da kala daya ba.

Kara karanta wannan

An soki Barau Jibrin kan karbar mutane zuwa APC alhali ana kukan kuncin rayuwa

Yadda aka illata Otedola da Dangote

A wani labarin, kun ji cewa Femi Otedola ya koka kan yadda gwamnatin marigayi Umaru Yar'Adua ta dakile shi da Aliko Dangote.

Odetola ya bayyana cewa sun shirya mallakar matatun mai a Kaduna da Port Harcourt amma shugaba Yar'Adua ya rusa tsarin.

Ya ce sun kulla yarjejeniya na siyan hannun jari a matatun biyu a mulkin tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo kafin ya sauka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.