TUC Ta Yi Fatali da Ƙarin Farashin Man Fetur, Ta Aika Sakon Gaggawa ga Bola Tinubu

TUC Ta Yi Fatali da Ƙarin Farashin Man Fetur, Ta Aika Sakon Gaggawa ga Bola Tinubu

  • Ƙungiyar kwadago TUC ta yi fatali da ƙarin farashin man fetur a Najeriya, ta ce duk wahalar a kan ma'aikatan kasar za ta ƙare
  • Shugaban TUC, Festur Osifo ya bukaci gwamnatin tarayya ta soke ƙarin nan take kana ta maida hankali wajen farfaɗo da Naira
  • Kwamared Osifo ya ce ƙungiyar TUC za ta ci gaba da fafutukar kare haƙƙi da muradan ma'aikata domin tabbatar da walwalarsu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Kungiyar ‘yan kwadago (TUC) ta yi fatali da karin farashin man fetur da aka yi kwanan nan daga N568 zuwa sama da N800 a Najeriya.

TUC ta bayyana cewa wannan ƙarin babbar illa ce domin zai kara jefa ma'aikata cikin ƙangin talauci da wahalar rayuwa.

Kara karanta wannan

Gwamna ya shiga tsaka mai wuya, jam'iyya ta fara shirin ɗaukar mataki a kansa

Shugaban TUC, Kwamared Festus Osifo.
TUC ta buƙaci gwamnatin tarayya ta soke ƙarin da ta yi a farashin man fetur Hoto: Festus Osifo
Asali: Facebook

Channels tv ta rahoto cewa hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da shugaban TUC na ƙasa, Festus Osifo ya fitar ranar Laraba, 4 ga watan Satumba, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

TUC ta aika saƙo ga Shugaba Tinubu

Shugaban TUC ya yi kira ga gwamnatin tarayya ƙarƙashin Bola Ahmed Tinubu ta gaggauta janye wannan matakin da ta ɗauka na kara farashin mai.

Ya buƙaci ta maida hankali wajen bullo da tsare-tsaren da za su karawa Naira daraja da yaye wahala da kuncin da ƴan Najeriya suke ciki, rahoton Leadership.

Kwamared Festua Osifo ya ce ɗaukar irin waɗannan matakin ba tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki ba ya kara nuna rashin damuwar gwamnati da walwalar jama'a.

Ƙungiyar kwadago za ta kare walwalar ma'aikata

"Muna kira ga gwamnati da ta gaggauta soke ƙarin, kana ta ɓullo da manufofin da za su karfafa Naira da daukar kwararan matakai don rage radadin da ‘yan Najeriya ke ciki.

Kara karanta wannan

Farashin Fetur: Fadar shugaban ƙasa ta mayar da martani ga kungiyar ƙwadago NLC

"TUC ba za ta yi ƙasa a guiwa ba wajen kare haƙƙi da muradan ma'aikata a Najeriya kuma za ta ci gaba da gwagwarmayar tabbatar da adalci, albashi da wurin aiki mai kyau ga ma'aikata," in ji Osifo.

NLC ta ce Tinubu ya yaudari ƴan Najeriya

A wani rahoton kuma ƙungiyar ƙwadago (NLC) ta yi martani mai zafi kan ƙarin kuɗin man fetur da aka yi a ƙasar nan a farkon makon nan

NLC ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu ya yaudare ta tare da sauran ƴan Najeriya sakamakon ƙarin kuɗin fetur da aka yi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262