Farashin Man Fetur Ya Ƙara Tashi, Kowace Lita Ta Haura N1,000 a Kano

Farashin Man Fetur Ya Ƙara Tashi, Kowace Lita Ta Haura N1,000 a Kano

  • Ƙarancin man fetur ya ƙara tsananta yayin da farashin lita ya kai N1,200 a gidajen man ƴan kasuwa a jihar Kano ranar Talata
  • Rahotanni sun nuna cewa farashin ya tashi zuwa N904 a gidajen man kamfanin NNPCL, masu ababen hawa sun yi layi suna jira
  • Wani ma'aikaci a ɗaya daga cikin gidan man NNPC ya ce sun wayi gari ne da ƙarin amma har yanzu suna jiran a ba su umarni

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Farashin litar man fetur ya tashi zuwa N1,200 a mafi yawan gidajen mai a birnin Kano yayin da gidajen man NNPC ke sayarda lita kan N904.

Rahotanni sun nuna ƙarancin man ya kara tsananta a sassan ƙasar nan, masu ababen hawa sun yi dogon layi a gidajen mai musamman na NNPC.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun jefa bama bamai a hedkwatar ƴan sanda, sun tafka ta'asa

Farashin fetur ya tashi a Kano.
Farashin litar Fetur ya taɓo N1,200 a gidajen man ƴan kasuwa a Kano Hoto: NNPCL
Asali: Getty Images

Yadda NNPC ya ƙara farashin man fetur

Wani ma'aikaci a ɗaya daga cikin gidajen man NNPC ya shaidawa Daily Trust cewa suna jiran umarni ne daga sama gabanin fara sayar da fetur a sabon farashi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ma'aikacin wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce:

"Mun fito aiki yau (Talata) da safe muka kunna inji ba zato muka ga an yi ƙari, yanzu haka dai muna jiran umarni kafin mu fara sayarwa," in ji shi.

Ƴan Najeriya sun koka da ƙarin kuɗin fetur

Wani mai mota, Isah Muhammad wanda ke cikin dogon layin ababen hawa ya nuna damuwarsa kan ƙarin farashin da aka yi.

"Ina muka dosa a kasar nan? Ina ake son talaka ya sa ransa? Abin da ban haushi, muna gani ake mana haka," in ji shi.

Har ila yau wani direban mota duk dai a Kano, Ibrahim Saleh ya tuna lokacin da yake sana'ar bunburutu a lokacin mulkin marigayi Ƴar'adua.

Kara karanta wannan

Ana murna matatar Dangote ta fara samar da fetur, NNPCL ya kara farashin litar mai

"Ina tuna lokacin da nake sana'ar sayar da mai, lokacin ana sayar da lita N95. Wata rana mun je sayen mai a lokacin mulkin Ƴar'adua, kawai aka hana ba da mai.
"Duk mun saduda za a ƙara kuɗin mai amma kawai suka rage shi zuwa N65, ba na manta wannan, har yanzun ina tuna abin a rayuwata."

Legit Hausa ta tuntuɓi wani mazaunin Hotoro a jihar Kano, Sanusi Isiyaku, wanda ya tabbatar mana da halin da ake ciki musamman dogon layin ababen hawa a gidan mai.

Sanusi ya ce mutane na cikin wahala da tsadar rayuwa, wannan ƙarin da aka yi zai ƙara jefa talakawa cikin ƙaƙanikayi.

Ya ce:

"Na yi mamakin layin da na gani a gidan man NNPC da safe, duk da ana samun layi idan akwai mai amma na yau ya fi muni, ina ake son mu sa kanmu ne.
"Sun cire tallafi mun haƙura to a samar mana da man mana, da kuɗinmu fa zamu siya. Mun wayi gari da labari mai daɗi na fara aikin matatar Ɗangote, taya tsada za ta biyo baya?"

Kara karanta wannan

Ganduje: Tinubu, Buhari da wasu ƙusoshin APC za su yanke makomar shugaban APC

Matatar Ɗangote ta gabatar da sumfurin mai

Kuna da labarin matatar man Ɗangote ta gabatar da sumfurin farko na man fetur ɗin da ta tace wanda zai shiga kasuwa nan gaba kaɗan.

Alhaji Aliko Ɗangote shi ne ya bayyana sumfurin yayin zantawa da ƴan jarida ranar Talata da safe a matatar da ke a jihar Legas.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262