Ana Murna Matatar Dangote Ta Fara Samar da Fetur, NNPCL Ya Kara Farashin Litar Mai

Ana Murna Matatar Dangote Ta Fara Samar da Fetur, NNPCL Ya Kara Farashin Litar Mai

  • Ana murna matatar Aliko Dangote ta fara samar da man fetur, kamfanin man NNPCL ya kara farashin mai a gidajensa
  • Wasu gidajen sun kara kudin litar mai daga N568 zuwa N855 har N897 a wasu wuraren da rahotanni suka tabbatar a yau
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa tun bayan cire tallafin mai a kasar baki daya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku

FCT, Abuja - Kamfanin mai na NNPCL ya kara farashin litar mai a mafi yawan wurare a fadin Najeriya.

A mafi yawan gidajen mai musamman na kamfanin NNPCL, an kara kuɗin har zuwa N855 kan farashin lita da a baya ake siyarwa N568.

Kara karanta wannan

Farashin man fetur ya ƙara tashi, kowace lita ta haura N1,000 a Kano

Kamfanin NNPCL ya kara farashin litar mai a Najeriya
Kamfanin NNPCL ya daga farashin litar mai daga N568 zuwa N897. Hoto: NNPCL Limited.
Asali: UGC

NNPCL ya sake daga farashin litar mai

Daily Trust ta tabbatar da cewa an kara farashin litar ne yayin da matatar Dangote ke shirin fara samar da fetur a Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu gidajen mai na musamman na NNPCL suna siyar da litar har N897 daga N568 a baya.

Hakan na zuwa ne kwana biyu bayan matatar Dangote ta tabbatar da fara fitar da man fetur a kasar domin saukakawa al'umma.

Wane martani NNPCL ya yi kan farashin?

Sai dai zuwa yanzu kamfanin bai fitar da sanarwar a hukumance kan karin farashin ba kamar yadda ake yadawa, cewar rahoton Vanguard.

Karin farashin na zuwa ne awanni 48 bayan kamfanin ya yi korafin yana bin masu shigo da mai kasar bashin N6bn.

Hakan ya biyo bayan karyata zancen a lokuta da dama a baya kafin tabbatar da hakan a ranar Lahadi 1 ga watan Satumbar 2024.

Kara karanta wannan

"Shugaba Tinubu ne zai kayyade farashi," Dangote ya fadi lokacin fadan kudin litar fetur

Tattaunawar Legit Hausa da mai saida mai

Wakilin Legit Hausa ya zagaya gidajen mai da dama a Gombe inda ya tarar a kulle.

Sai dai ya samu tabbacin cewa an fara ba da man daga baya ne suka kulle saboda tashin farashi.

Wani mai siyar da mai mai suna Abdulmajid Muhammad ya tabbatar da cewa sun siyar da litar kan N970.

Ya ce daga bisani an kulle gidan man inda ya ce akwai hasashen gobe za su fara siyarwa kan N1,200 ko fiye da haka.

Matatar Dangote ta fara samar da fetur

A wani labarin, kun ji cewa matatar man attajiri Aliko Dangote ta bayyana tsarin yadda za ta siyar da fetur ga 'yan kasuwa.

Matatar ta tabbatar da cewa za ta fitar man kasashen ketare idan har 'yan kasuwa daga Najeriya suka ki siyan man.

Mataimakin shugaban bangaren man da kuma gas, Devakumar Edwin shi ya bayyana haka a jiya Litinin 2 ga watan Satumbar 2024.

Kara karanta wannan

Ganduje: Tinubu, Buhari da wasu ƙusoshin APC za su yanke makomar shugaban APC

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.