Matawalle Ya Fadi Shirin Kawo Karshen Bello Turji da Sauran Manyan 'Yan Bindiga

Matawalle Ya Fadi Shirin Kawo Karshen Bello Turji da Sauran Manyan 'Yan Bindiga

  • Ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle zai jagoranci gagarumin shirin kawo ƙarshen ƴan bindigan da suka addabi yankin Arewa maso Yamma
  • Matawalle ya umarci babban hafsan tsaro na ƙasa da sauran hafsoshin tsaro su koma Sokoto domin kawo ƙarshen ƴan bindiga
  • Ministan wanda shi ma zai kasance a Sokoto, ya sha alwashin kawo ƙarshen ƴan bindigan da suka addabi mutanen yankin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle, ya sanar da wani gagarumin shiri na yaƙi da ƴan bindiga.

Shirin na ƙoƙarin kawo ƙarshen ƴan bindigan za a yi shi ne kan miyagun da suka addabi jihohin Sokoto, Zamfara, Katsina, da Kebbi.

Matawalle ya sha alwashi kan 'yan bindiga
Matawalle ya magantu kan rashin tsaro a jihohin Arewa Hoto: @BelloMatawalle1
Asali: Twitter

Daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar tsaro, Henshaw Ogugbike ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, cewar rahoton jaridar The Punch.

Kara karanta wannan

Malami ya bayyana hanya 1 da za a iya kayar da Shugaba Tinubu a zaɓen 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matawalle ya koka kan rashin tsaro

Matawalle ya nuna matuƙar damuwarsa kan rashin tsaron da ake fama da shi a yankin Arewa maso Yamma, rahoton tashar Channels tv ya tabbatar.

Ya bayyana cewa an umurci babban hafsan tsaron ƙasa da sauran manyan hafsoshin soji da su haɗu da shi a Sokoto, inda nan ne hedkwatar rundunar da ke yaƙi da ƴan bindiga a yankin.

Wane alwashi ministan ya sha kan Bello Turji?

Ministan ya sha alwashin cewa gwamnatin tarayya za ta yi amfani da duk abin da ya dace domin fatattakar shugaban ƴan bindiga nan Bello Turji da tawagar mayaƙansa.

"Ba za mu ƙyale waɗannan ƴan bindigan da ƴan ta’adda su ci gaba da muzgunawa mutanenmu ba."
"Lokacinsu ya zo ƙarshe. Za mu raunana sansanonin su, mu maido da zaman lafiya a cikin al’ummominmu."

Kara karanta wannan

Zargin ta'addanci: Shugaban NLC ya bar wurin ƴan sanda, ya koma hedkwatar ƴan kwadago

- Bello Matawalle

Matawalle wanda zai kasance tare da hafsoshin tsaron, ya tabbatarwa al’ummar Sokoto, Zamfara, Katsina, da Kebbi cewa, rundunar sojoji ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba a ƙoƙarin kawar da ƴan bindiga daga yankin.

Ya kamata a kawo ƙarshen ƴan bindiga

Muhammad Auwal ya shaidawa Legit Hausa cewa tun tuni ya kamata a ce gwamnati ta tashi tsaye ta kawo ƙarshen ƴan bindiga.

Ya bayyana cewa matakin da gwamnatin ta ɗauka zai nuna cewa da gaske take yi wajen kawo ƙarshen matsalar rashin tsaron.

"Idan da gaske suke yi za su koma can su tare, ina ganin ba za a daɗe ba za a kawo ƙarshen miyagun nan. Ƴan ta'addan an san inda suke, kamata ya yi a je a rufar musu kawai."

- Muhammad Auwal

Matawalle ya fusata kan kisan Sarkin Gobir

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle ya yi Allah wadai da kisan hakimin Gatawa dake ƙaramar hukumar Sabon Birni a Sakkwato wanda aka fi sani da Sarkin Gobir.

Matawalle ya bayyana kisan sarkin Gobir, Muhammad Isa Bawa a matsayin ɗanyen aiki na rashin imani, inda ya ce duk mai hannu a kisan zai ɗanɗana kuɗarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng