Shugaba Bola Tinubu Ya Lula Zuwa Ƙasar China, Zai Tsaya a Wata Ƙasa a kan Hanya

Shugaba Bola Tinubu Ya Lula Zuwa Ƙasar China, Zai Tsaya a Wata Ƙasa a kan Hanya

  • Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis, ya bar babban birnin tarayya Abuja zuwa ƙasar China inda zai kai ziyarar aiki
  • Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, ya ce Tinubu zai tsaya a UAE
  • Wannan ziayara na zuwa ne a daidai lokacin da wani kamfanin China ya ƙwace jiragen shugaban kasa a ƙasar Faransa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya bar babban birnin tarayya Abuja zuwa ƙasar Sin watau China, inda zai kai ziyarar aiki.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ya ce Bola Tinubu zai ɗan tsaya a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) kafin daga bisani ya wuce China.

Kara karanta wannan

Jigo a APC ya hango illar hana dalibai rubuta WAEC da NECO, ya ba Tinubu shawara

Shugaban kasa Bola Tinubu.
Shugaban Ƙasa Tinubu ya kama hanyar zuwa ƙasar China Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Twitter

Cif Ngelale ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook yau Alhamis, 29 ga watan Agusta, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ayyukan da Bola Tinubu zai yi a China

"Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai tashi daga Abuja ranar Alhamis, 29 ga watan Agusta, 2024 zuwa birnin Beijing na kasar Sin domin ziyarar aiki.
"Shugaban zai tsaya wata ƴar taƙaitacciyar ziyara a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE). Yayin ziyarar aiki a Sin, Tinubu zai gana da Shugaba Xi Jinping da kuma ƴan kasuwa.
"A gefe guda kuma shugaban kasarzai halarci taron tattaunawa kan alaƙar China da nahiyar Afirka," in ji sanarwar.

Kamfanin China ya ƙwace jiragen Najeriya

Wannan ziyara ta Tinubu na zuwa ne a daidai lokacin da wani kamfani mai suna Zhongshan Fucheng daga China ya kwace jiragen Najeriya.

Kwanan nan wata kotu a Faransa ta yanke hukunci kan taƙaddamar, inda ta ba kamfanin izinin kama jiragen shugaban kasa mallakar gwamnatin Najeriya.

Kara karanta wannan

Babban hafsan tsaron Najeriya ya kai ziyara Jamhuriyar Nijar, bayanai sun fito

Mai girma Shugaba Tinubu ya tafi wannan ziyarar aiki tare da rakiyar manyan ƙusoshin gwamnatin Najeriya.

Da zarar an gama taron da za a yi, zai kamo hanyar dawowa birnin tarayya Abuja.

Tinubu ya dawo da tallafin lantarki

Kuna da labarin gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta maido tallafin wutar lantarki da kashi 50% ga dukkan asibitocin gwamnati a fadin ƙasar nan.

Ministan lafiya da walwalar al'umma, Dakta Tunji Alausa ne ya bayyana haka yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar Kaduna.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262