Hukumar DIA Ta Kama Ɗan Sanda da Wasu Mutane 19 Bisa Zargin Ta'addanci a Najeriya

Hukumar DIA Ta Kama Ɗan Sanda da Wasu Mutane 19 Bisa Zargin Ta'addanci a Najeriya

  • Hukumar tattara bayanan sirri DIA za ta ci gaba da tsare ɗan sanda da wasu da ake zargi da taimakawa ƴan ta'adda a Najeriya
  • Wata babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ce ta amince DIA ta ci gaba da tsare waɗanda ake zargi na tsawon kwanaki 30
  • Mai shari'a Peter Lifu ya yanke wannan hukunci a karar da hukumar DIA ta shigar ta hannun lauyanta watau S.A Aminu Esq.

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ba hukumar leken asiri (DIA) ta ƙasa izinin ci gaba da tsare wani mataimakin Sufeton ‘yan sanda (ASP) A. A. Babangida da wasu mutane 19.

Kara karanta wannan

Kaduna: Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje sama da 200, SEMA ta ɗauki mataki

Kotun ta amince hukumar DIA ta tsare su ne bisa zargin suna da hannu a hare-haren ƴan bindiga, garkuwa da mutane da ayyukan ta'addanci.

Yan sandan Najeriya.
Kotu ta amince a ci gaba da tsare dan sanda da wasu mutum 19 da ake zargi da ta'addanci Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Twitter

Jerin waɗanda DIA ke zargi da ta'addanci

The Nation ta tattaro cewa sauran waɗanda aka kama baya ga ɗan sandan sun haɗa da Usman Idris, Abu Safiyanu, Alhassan Idris, Sahada Ishaka da Abubakar Bello.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran su ne Yahaya Abdullahi, Haruna Salisu, Mohammed Muazu, Nura Idris, Alhaji Manu Mohammed, Umar Lamu da wani Abubakar Mandara.

Har ila yau akwai Suleiman Mohammed, Alhaji Madayi, Alhaji Amodu Oghewe da Uzoma Aghaoyibo.

Mai shari’a Peter Lifu ya yanke wannan hukuncin ne a karar da DIA ta shigar mai lamba FHC/ABJ/CS/1146/2024 ta hannun lauyanta S.A Aminu.

Kotu ta yanke hukunci kan bukatar DIA

Kotun ta umarci DIA ta ci gaba da tsare ASP Babangida da sauran waɗanda ake zargi na tsawon kwanaki 30 don ba jami’an tsaron damar kammala binciken da suke yi.

Kara karanta wannan

Ana fama da yunwa, ambaliyar ruwa ta yi ɓarna a gonakin mutane a jihohi 2 na Arewa

Hukumar DIA ta bayyana cewa ta kama ɗan sandan ne tun a watan Yuni kuma har yanzun yana tsare a hannunta.

Ta kuma zargi dan sandan da taimakawa ‘yan Boko Haram da ‘yan bindiga da ‘yan kungiyar ISWAP wajen gudanar da ayyukan ta’addanci a sassan kasar nan.

DIA ba ta samu yadda ta so a kotu ba

Tun farko dai lauyan hukumar leƙen asiri DIA, Aminu ya buƙaci kotu ta amince a ci gaba da tsare waɗanda ake zargin na tsawon watanni uku.

Mai shari’a Lifu ya ki amincewa da bukatar kwanaki 90 saboda wadanda ake zargin sun shafe watanni uku a tsare, kamar yadda Punch ta kawo.

Janar Musa ya kai ziyara Nijar

A wani rahoton kuma babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya ziyarci takwaransa na Jamhuriyar Nijar, Janar Mousa Barmo.

Muƙaddashin daraktan yaɗa labarai na tsaro, Birgediya Janar Tukur Gusau ne ya sanar da haka ga manema labarai ranar Laraba a Abuja.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262