Shugaban Majalisa Ya Gano Hanyar Magance Rikicin Manoma da Makiyaya

Shugaban Majalisa Ya Gano Hanyar Magance Rikicin Manoma da Makiyaya

  • Shugaban majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas ya bayyana cewa sauyin yanayi ya ta'azzara rikicin manoma da makiyaya
  • Rt. Hon. Abbas ya bayyana haka ne yayin taron masu ruwa da tsaki wanda kwamitin muhalli na majalisa ya shirya
  • Ya bayyana cewa dole ne a dauki dabarun zamanantar da kiwo da noma domin rage rikici tsakanin masu noma da kiwo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Benue - Kakakin majalisar wakilai, Hon.Tajuddeen Abbas ya bayyana cewa karuwar sauyin yanayi ya kara jawo rikicin manoma da makiyaya a kasar nan.

Kakakin ya bayyana haka ne a taron masu ruwa da tsaki inda aka nuna wani shirin fim kan sauyin yanayi da rikicin manoma da makiyaya a jihar Binuwai.

Kara karanta wannan

Kasuwancin Arewa zai habaka, tashar tsandaurin Kebbi ta bude ofishi a Kano

Tajuddeen
Majalisar wakilai ta magantu kan rikicin manoma da makiyaya ta hanyar amfani da dabarun zamani Hoto: House of Representatives, Federal Republic of Nigeria
Asali: Facebook

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa Hon. Tajuddeen Abbas ya samu wakilcin dan majalisa mai wakiltar Makurdi/Guma a jihar Binuwai, Hon. Dickson Takighir.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce yadda ake cigaba da amfani da tsofaffin dabarun kiwo na daga cikin matsalolin da ke jawo saɓani tsakanin manoma da makiyaya.

Hanyar magance rikicin manoma da makiyaya

Majalisar wakilai ta bayyana cewa dole a zamanantar da noma da kiwo domin magance matsalar da ake samu tsakanin masu sana'ar biyu.

Voice of Nigeria ta wallafa cewa kakakin majalisa, Tajuddeen Abbas da ya bayyana haka, ya ce sai manoma da makiyaya sun yi koyi da tsarin cigaba domin bunkasa sana'o'insu.

Ana son magance rikicin manoma da makiyaya

Kakakin majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas ya ce gwamnatin tarayya da majalisa na son magance rikicin manoma da makiyaya.

Ya ce gwamnatin Bola Tinubu ta samar ma'aikatar kula da dabbobi domin zamanantar da kiwo.

Kara karanta wannan

Kwara: Ana cikin halin kunci, dattijuwa mai shekara 54 ta haifi jarirai 11, miji ya kidime

Fada ya barke tsakanin manoma da makiyaya

A baya mun ruwaito cewa rikici ya barke tsakanin manoma da.makiyaya bayan zargin an kashe wani manomi a Gbagyi a karamar hukumar Bosso da ke Neja.

An ce makiyayan sun kashe manomin ne bayan ya yi masu magana kan barin dabbobinsu sakaka a cikin gonarsa, lamarin da ya sa mazauna Gbagyi su ka yi ramuwar gayya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.