Jigawa: Mai Shayi Ya Lakaɗawa Matashi Duka Har Lahira Kan Ɓatan Indomi da Burodi

Jigawa: Mai Shayi Ya Lakaɗawa Matashi Duka Har Lahira Kan Ɓatan Indomi da Burodi

  • Wani mai shayi a kauyen Sararai da ke ƙaramar hukumar Dutse a Jigawa ya kashe matashi ɗan shekara 20 kan zargin satar indomi da burodi
  • Ƴan sanda sun kama wanda ake zargi, Abdulrashibu Ya'u kuma ya amsa laifin, ya ce mamacin ya matsa masa da sata
  • Makotan mai shayin sun bayyana cewa wanda ake zargin ya ɗaure matashin, ya riƙa bugunsa da itace har sai da ya daina motsi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Jigawa - Wani mai shayi ɗan kimanin shekara 40 a duniya, Abdulrashibu Ya’u, ya yiwa wani matashi dukan tsiya har lahira a jihar Jigawa.

Lamarin ya auku ne a kauyen Sararai da ke yankin Jigawar Tsada a ƙaramar hukumar Duts a jihar da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

Kara karanta wannan

"Ba mu da labari," Ƴan sanda su yi magana kan sace mutane 150 bayan kisan Sarkin Gobir

Yan sandan Najeriya.
Yan sanda sun kama.mai shayi bisa zargin kashe wani matashi a Jigawa Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Twitter

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa an zargi mamacin mai suna, Hassan Garba, ɗan shekara 20 da satar burodi, madara, indomi da kuma man fetur.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jigawa: Yadda mai shayi ya yi kisa

Wannan ya sa mai shayin ya ɗaure matashin, ya dinga bugunsa da icce har sai da ya mutu, kamar yadda Punch ta tattaro.

Take bayan samun rahoton, ƴan sanda suka kai ɗauki wurin, suka kama wanda ake zargi kana suka garzaya da Hassan Asibiti, daga zuwa likitoci suka ce ya mutu.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da lamarin yayin hira da ƴan jarida a Dutse. 

Wane mataki ƴananda suka ɗauka?

Ya ce Abdulrashibu Ya’u ya amince da aikata laifiin, inda ya ce yawan sace-sacen da Hassan ke masa ne ya tunzura shi kuma ya sha kai ƙararsa wurin iyayensa.

Kara karanta wannan

'Dalilin da ya sa Atiku, Kwankwaso da Obi ba ba su iya kayar da Tinubu a 2027 ba'

DSP Lawan ya ce mai shayin ya ɗaure matashin cikin fushi da igiya, ya rinƙa dukansa da sanda har ya ce ga garinku nan.

Ya ce makwabta sun ji kukan Hassan Garba na neman agaji amma sun kasa shiga tsakani har sai da jami’an ‘yan sanda suka ƙariso.

"Da zaran mun kammala bincike za mu gurfanar da mai shayin a gaban kotu domin a hukunta shi daidai da laifinsa," in ji Lawan Shiisu.

Surukar Nuhu Ribadu ta rasu

A wani rahoton Allah ya yiwa, Hajiya Ummu Iya Abubakar, surukar Nuhu Ribadu rasuwa ranar Talata, 27 ga watan Agusta, 2024

Iyalan marigayyar ne suka tabbatar da hakan a wata sanarwa da suka fitar, sun ce za a yi mata janaza a babban masallacin ƙasa da ke Abuja bayan Azahar

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262