Edo 2024: Dan Takarar Gwamna Ya Shiga Tashin Hankali, 'Yan Bindiga Na Farautarsa

Edo 2024: Dan Takarar Gwamna Ya Shiga Tashin Hankali, 'Yan Bindiga Na Farautarsa

  • Hon. Udoh Oberaifo, dan takarar gwamnan jihar Edo karkashin jam'iyyar AAC ya ce masu garkuwa da mutane na farautarsa
  • Dan takarar gwamnan a zaben jihar Edo na ranar 21 ga watan Satumban 2024 ya ce sau uku ana farmakarsa wajen yakin neman zabe
  • Hon. Udoh ya kuma yi ikirarin cewa rundunar 'yan sanda ta janye jami'an tsaron da ke ba shi kariya duk da cewa ya cike ka'idoji

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Edo - Gabanin zaben gwamnan Edo a ranar 21 ga Satumba, 2024, dan takarar jam’iyyar AAC, Udoh Oberaifo ya ce an yi yunkurin yin garkuwa da shi har sau uku.

Da yake zantawa da manema labarai a birnin Benin, Udoh ya kuma yi zargin cewa an lalata allunan yakin neman zabensa a birnin.

Kara karanta wannan

Sarkin Gobir: Ƴan Arewa sun fusata, sun kawo hanyoyin maganin yan bindiga

Dan takarar gwamnan Edo na AAC ya yi magana kan hare-haren da ake kai masa
Edo 2024: Dan takarar AAC ya ce masu garkuwa da mutane na farautarsa.
Asali: Original

An yi yunkurin kashe Udoh

Ya ce ya dade yana gudanar da yakin neman zabensa da nufin yiwa jama’a hidima amma abubuwan da suka faru a baya-bayan nan sun fara ba shi tsoro, inji rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“A ‘yan kwanakin nan, na fuskanci kalubale na matsalar tsaro. Sau uku ina tsallake tarkon masu garkuwa da mutane a lokutan da na fita yakin neman zabe.
"Kuma wannan ba wai farmakin gaba gadi ba ne, na tabbata ana farmaka ta ne domin a ga baya na, ko a sanya mun tsoro, ko a kawo tasgaro ga shirin takara ta."

- A cewar Hon. Udoh.

An janyewa Udoh jami'an tsaro

Jaridar Independent ta ruwaito Hon. Udoh ya yi ikirarin cewa an janye jami’an tsaron da ke gadinsa duk da daukar matakan da suka dace domin magance hakan ta hanyar bin tsarin doka.

Kara karanta wannan

Daga karin kumallo, uwa da ƴaƴanta 3 sun rasu a wani yanayi mai ban tausayi

A cewar Hon. Udo:

“Na aikawa sufeta janar na ‘yan sanda takarda, kuma na gana da mataimakin sufeta Janar a Abuja a makon da ya gabata, amma abin ya ci tura duk da alkawarin da aka mun."

Don haka ya yi kira ga hukumar ‘yan sanda da ta dauki matakin gaggawa domin maido da jami'an tsaronsa tare da tabbatar da cewa ba a sake yin wani yunkuri na kashe shi ba.

Edo: PDP ta ki ajiye Ighodalo

A wani labarin, mun ruwaito cewa jam'iyyar PDP ta ce lallai Dakta Asue Ighodalo ne dan takararta na gwamnan Edo, a zaben gwamnan jihar da za a gudanar a watan Satumbar 2024.

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ce ta soke zaben PDP na watan Fabrairun 2024 saboda an cire sunayen wasu wakilai 378 ba bisa ka'ida ba, sai dai jam'iyyar ta yi watsi da wannan hukunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.