Jami'an Tsaro Sun Tunkari Ƴan Bindiga, An Ceto Ɗaliban Jami'o'in Arewa 2 da Aka Sace

Jami'an Tsaro Sun Tunkari Ƴan Bindiga, An Ceto Ɗaliban Jami'o'in Arewa 2 da Aka Sace

  • Rahotanni sun tabbatar da cewa an ceto ɗalibai likitoci 20 waɗanda ƴan bindiga suka yi garkuwa da su a makon da ya shige
  • Majiyoyi sun bayyana cewa jami'an tsaro da suka kunshi ƴan sanda, sojoji da DSS ne suka kai samame kuma Allah ya ba su nasara a Benuwai
  • Ɗaliban dai sun fito ne daga Jami'ar Maiduguri a Borno da Jami'ar Jos da ke Filato, a hanyar zuwa Enugu suka faɗa tarkon masu garkuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Benue - Ɗaliban likitanci 20 da ƴan bindiga suka yi garkuwa da su kusan mako guda da ya wuce sun shaƙi iskar ƴanci.

Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa jami'an tsaron haɗin guiwa ne suka yi nasarar ceto ɗaliban waɗanda suka fito daga Jami'ar Maiduguri da Jami'ar Jos.

Kara karanta wannan

DHQ: Sojoji sun hallaka ƴan ta'adda sama da 150, sun kama wasu 302 a Najeriya

Sufetan yan sanda, IG Kayode.
Dalibai 20 da ke karatun zama kwararrun likitoci sun kubuta daga hannun ƴan bindiga Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro ne ya jagoranci aikin ceto ɗaliban da ke ƙaratun zama likita.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda jami'an tsaro suka ceto ɗaliban

Dakarun tsaro da suka haɗa da jami'an ƴan sanda, jami'an hukumar tsaron farin kaya DSS da sojoji cikin shiri da kayan aiki, su ne suka kaddamar da Oepration ɗin.

Bugu da ƙari, gwamnatin jihar Benuwai karƙashin jagorancin Gwamna Hyacinth Alia ta ba jami'an goyon baya har suka yi nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai likitocin ne a kan babbar hanyar Otukpo zuwa Enugu a karamar hukumar Otukpo ta jihar Benuwai a Arewa ta Tsakiya.

Lamarin ya faru ne a lokacin da suke hanyar zuwa jihar Enugu da ke Kudu maso Gabas domin halartar wani taro a makon jiya.

Kara karanta wannan

Boko Haram zuwa 'yan bindiga: Manyan sarakuna 3 da 'yan ta'adda suka hallaka a Najeriya

Tawagar IGP sun dura Benuwai

Kamar yadda Punch ta ruwaito, tawagar dakarun sifeyan ƴan sanda na ƙasa sun isa jihar Benuwai a ranar Litinin, 19 ga watan Agusta, kuma suka wuce Otukpo domin ceto ɗaliban.

A halin yanzun dai majiyoyi daga hukumomin tsaro sun tabbatar da ceto ɗaliban daga hannun miyagu.

Sojoji sun hallaka ƴan ta'adda 171

A wani rahoton kuma dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe ƴan ta'adda 171 tare da ceto mutane 134 da aka yi garkuwa da su a mako guda

Hedkwatar tsaron ta ƙasa DHQ ta bayyana cewa sojojin sun kwato manyan bindigu da alburusai daga hannun ƴan ta'adda.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262