Bayan Kamfanin China Ya Kwace Kadarori a Waje, an Kai Gwamnatin Tinubu Kotu a Gida

Bayan Kamfanin China Ya Kwace Kadarori a Waje, an Kai Gwamnatin Tinubu Kotu a Gida

  • Gwamnatin tarayya ta fitar da sanarwa kan babbar hanyar Legas zuwa Kalaba bayan al'umma sun maka ta a kotu kan aikin
  • Ministan ayyuka, David Umahi ya bayyana haka a ranar Alhamis a Abuja kuma yayi karin haske kan matsalolin da kea fuskanta
  • Mutanen da aikin hanyar zai shafa sun maka gwamanti a kotu ne kan cewa kudin da aka ba su domin amfani da wurarensu ya yi kadan

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Al'ummar da aikin titin Legas zuwa Kalaba zai shafa sun maka gwamnatin Bola Tinubu a kotu.

Mutanen sun koka ne kan cewa ba a biya su kudin wurarensu da aka karba domin yin aikin yadda ya kamata ba.

Kara karanta wannan

Ana jimamin kisan sarkin Gobir, 'Yan bindiga sun kashe manoma 13 a Arewacin Najeriya

Lagos Calaba
An maka gwamnatin tarayya a kotu kan aikin titi. Hoto: @drpenking
Asali: Twitter

Jaridar Punch ta wallafa cewa ministan ayyuka, David Umahi ya ce ba abin da zai hana gwamnati fara aikin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu da aikin titin Legas-Kalaba

Aikin titin Legas zuwa Kalaba na cikin manyan ayyuka da Bola Tinubu ta dauko yi a Najeriya wanda za a kammala cikin shekaru takwas.

Titin zai kutsa ta cikin jihohi da dama kuma zai laƙume N15tn ta inda mutane ke cewa za a kashe N4bn a duk kilo mita daya.

An maka gwamnatin Tinubu a kotu

Wasu da aka karbi filayensu sun nuna damuwa kan karancin kudin da aka biya inda suka nufi kotu domin neman a kara musu kudi.

Leadership ta wallafa cewa ministan ayyuka, David Umahi ya ce a yanzu haka suna cikin shari'a guda shida da mutanen suka maka su a kotu kan titin.

Kara karanta wannan

Bacin ciki: Jihohin Najeriya 6 da mutane 43 suka rasa rayukansu daga cin abinci

Aikin titin Legas zuwa Kalaba zai tsaya?

Ministan ayyuka, David Umahi ya ce waɗanda suka maka su a kotu kawai suna bata lokaci ne domin sun riga sun biya su yadda ya kamata.

Haka zalika Umahi ya ce ya sha fama da irin rikice rikicen a baya kuma ya yi nasara saboda haka ba ya kokonto kan cewa za su yi nasara.

Ministan Tinubu ya soki kamfanin titi

A wani rahoton, kun ji cewa Sanata David Umahi bai ji dadin aikin da ya gani a titin Amanwozuzu-Uzoagba-Eziama-Orie-Amakohia ba.

Ministan ayyukan na Najeriya ya yi kaca kacea da kamfanin Fig Fyne Construction Company da aka ba kwangilar bisa zargin yin aikin maras nagarta.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng