Bayan Kamfanin China Ya Kwace Kadarori a Waje, an Kai Gwamnatin Tinubu Kotu a Gida
- Gwamnatin tarayya ta fitar da sanarwa kan babbar hanyar Legas zuwa Kalaba bayan al'umma sun maka ta a kotu kan aikin
- Ministan ayyuka, David Umahi ya bayyana haka a ranar Alhamis a Abuja kuma yayi karin haske kan matsalolin da kea fuskanta
- Mutanen da aikin hanyar zai shafa sun maka gwamanti a kotu ne kan cewa kudin da aka ba su domin amfani da wurarensu ya yi kadan
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja - Al'ummar da aikin titin Legas zuwa Kalaba zai shafa sun maka gwamnatin Bola Tinubu a kotu.
Mutanen sun koka ne kan cewa ba a biya su kudin wurarensu da aka karba domin yin aikin yadda ya kamata ba.

Asali: Twitter
Jaridar Punch ta wallafa cewa ministan ayyuka, David Umahi ya ce ba abin da zai hana gwamnati fara aikin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tinubu da aikin titin Legas-Kalaba
Aikin titin Legas zuwa Kalaba na cikin manyan ayyuka da Bola Tinubu ta dauko yi a Najeriya wanda za a kammala cikin shekaru takwas.
Titin zai kutsa ta cikin jihohi da dama kuma zai laƙume N15tn ta inda mutane ke cewa za a kashe N4bn a duk kilo mita daya.
An maka gwamnatin Tinubu a kotu
Wasu da aka karbi filayensu sun nuna damuwa kan karancin kudin da aka biya inda suka nufi kotu domin neman a kara musu kudi.
Leadership ta wallafa cewa ministan ayyuka, David Umahi ya ce a yanzu haka suna cikin shari'a guda shida da mutanen suka maka su a kotu kan titin.
Aikin titin Legas zuwa Kalaba zai tsaya?
Ministan ayyuka, David Umahi ya ce waɗanda suka maka su a kotu kawai suna bata lokaci ne domin sun riga sun biya su yadda ya kamata.
Haka zalika Umahi ya ce ya sha fama da irin rikice rikicen a baya kuma ya yi nasara saboda haka ba ya kokonto kan cewa za su yi nasara.
Ministan Tinubu ya soki kamfanin titi
A wani rahoton, kun ji cewa Sanata David Umahi bai ji dadin aikin da ya gani a titin Amanwozuzu-Uzoagba-Eziama-Orie-Amakohia ba.
Ministan ayyukan na Najeriya ya yi kaca kacea da kamfanin Fig Fyne Construction Company da aka ba kwangilar bisa zargin yin aikin maras nagarta.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng