Gwamna Zulum Ya Cika Aiki, Tallafin Shugaba Tinubu Ya Isa Hannun Magidanta 10,000

Gwamna Zulum Ya Cika Aiki, Tallafin Shugaba Tinubu Ya Isa Hannun Magidanta 10,000

  • Kashin karshe na tallafin tireloli 20 da gwamnatin tarayya ta tura Borno ya isa hannun mutane a karamar hukumar Mafa
  • Gwamna Babagana Umaru Zulum ya rabawa magidanta 10,000 tallafin hatsi a ranar Talata, 20 ga watan Agusta, 2024
  • Zulum ya kuma raba tallafin tsabar kudi N150m ga mata domin su kama sana'a, sannan ya miƙa godiya ga Bola Tinubu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Borno - Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum ya rabawa magidanta 10,000 tallafin hatsin da gwamnatin tarayya ta turo jihar.

Gwamma Zulum ya kuma ciro N150m daga asusun gwamnatin Borno, ya rabawa mata domin yabawa kokarin gwamnatin tarayya duba da halin da ake ciki.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta yi bayani kan umarnin Tinubu na biyan 'kudin tallafin mai'

Gwamna Zulum.
Gwamna Zulum ya rabawa jama'a tallafin da Bola Tinubu ya turo Borno Hoto: Professor Babagana Umara Zulum
Asali: Twitter

The Nation ta tattaro cewa Farfesa Zulum ya rabawa magidanta wannan tallafi ne a ƙaramar hukumar Mafa da je jihar Borno.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da yake jawabi a wajen taron raba tallafin a garin Mafa a ranar Talata, Zulum ya ce hatsin shi ne kashin karshe na tireloli 20 da gwamnatin tarayya ta turo.

Bola Tinubu ya rabawa jihohi tirela 20

A makonnin baya gwamnatin tarayya ta sanar da cewa za ta ba kowace jiha da Abuja tallafin tirela 20 na shinkafa da kayan hatsi domin a rabawa talakawa.

Ministan yaɗa labarai, Muhammed Idris, ya ce an ɗauki wannan matakin ne domin sauke farashin abinci da kuma ragewa al'umma raɗaɗin ƙuncin rayuwa.

Gwamna Zulum ya yabawa gwamnatin Tinubu

Gwamna Zulum ya yabawa gwamnatin tarayya ƙarƙashin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa tallafin da take bai wa jama'a domin rage raɗaɗi, NTA News ta rahoto.

Kara karanta wannan

Atiku ya yi zazzafan martani ga Shugaba Tinubu kan dawo da tallafin man fetur

Kazalika gwamnan ya roƙi ƴan Najeriya da su ba Gwamnatin Bola Tinubu goyon bayan da take buƙata kuma su fahimci tsare-tsaren da ta ɗauko domin saita ƙasar nan.

Hakan a cewarsa, zai ba gwamnati a dukkan matakai damar aiwatar da karin tsare-tsare da manufofin da za su rage wahalhalun da jama’a ke ciki.

Gwamna ya tallafawa waɗanda suka yi haɗari

A wani rahoton kun ji Gwamnan jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu ya ware tallafin N30m ga waɗanda hatsarin jirgin ruwa ya rutsa da su a kauyen Dundaye.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa za ta bai wa iyalan mutum biyar da suka rasu a haɗarin N15m yayin da waɗanda suka tsira kuma za a ba su N15m.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262