Bayan Fadin Albashin Sanatoci, Kawu Sumaila Ya Yi Sabuwar Fallasa

Bayan Fadin Albashin Sanatoci, Kawu Sumaila Ya Yi Sabuwar Fallasa

  • Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila ya zargi tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Aremu Obasanjo da kawo cin hanci da rashawa a majalisa
  • Sanatan mai wakiltar Kano ta Kudu ya bayyana cewa Obasanjo ya kawo cin hanci a majalisar domin cimma ƙudirinsa na yin tazarce a karo na uku
  • Kalaman na Kawu Sumaila na zuwa ne a matsayin martani kan zargin da Obasanjo ya yi na cewa ƴan majalisar tarayya suna yanke abin da za a biya su

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdulrahman Kawu Sumaila ya zargi tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo da kawo cin hanci da rashawa a majalisar tarayya.

A makon da ya gabata ne Obasanjo ya zargi ƴan majalisun da ƙayyade albashi da alawus-alawus ɗinsu da kansu a yayin da ake fama da taɓarɓarewar tattalin arziƙi a Najeriya.

Kara karanta wannan

Albashin N21m: Majalisa ta bayyana gaskiya kan abin da ake biyan sanatoci

Kawu Sumaila ya zargi Obasanjo
Kawu Sumaila ya zargi Obasanjo da kawo cin hanci a majalisa Hoto: @AbdullahiSml55, @Oobasanjo_obj
Asali: Twitter

Kawu Sumaila ya caccaki Olusegun Obasanjo

A yayin wata tattaunawa da tashar Channels tv a ranar Alhamis, Kawu Sumaila ya caccaki kalaman na Olusegun Obasanjo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanatan wanda ya fito ya bayyana abin da ake ba shi duk wata a matsayin albashi, ya zargi Obasanjo da gurɓata wasu ƴan majalisa ta hanyar ba su cin hanci a lokacin mulkinsa.

Wane zargi Kawu Sumaila ya yi kan Obasanjo?

"Idan ana magana kan cin hanci da rashawa, Obasanjo ne ya kawo cin hanci a majalisar dokoki ta tarayya."
"Ina da shaida saboda gwamnatinsa da wasu na kusa da shi ne suka gurɓata wasu ƴan majalisun tarayya domin su yiwa kundin tsarin mulki kwaskwarima domin ya samu damar yin tazarce."

- Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila

Ɓoye haƙiƙanin abin da ake biyan sanatocin a matsayin albashi da alawus dai ya zama abin magana inda ake ta tafka muhawara a kai.

Kara karanta wannan

Sace takardun shari'a: Ganduje ya yi wa Gwamna Abba martani mai zafi

Albashin da ake biyan sanatoci duk wata

A wani labarin kuma, kun ji cewa alamu sun nuna cewa adadin albashin da ake biyan sanatoci 99 na majalisar dattawan Najeriya duk wata ya haura N2bn.

Wannan adadin bai ƙunshi albashin da ake biyan shugabannin majalisar su 10 ba, waɗanda har yanzu ba a san abin da suke karɓa ba duk wata.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng