Tinubu ya Fito da Salon Tsarin Tsaro a Arewa Domin Maganin Ƴan Bindiga

Tinubu ya Fito da Salon Tsarin Tsaro a Arewa Domin Maganin Ƴan Bindiga

  • Gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta fito da hanyar maganin yan bindiga da suka addabi jihohin Arewacin Najeriya
  • Tinubu ya dauki matakin ne biyo bayan yawaitar kai hare hare ga manoma da yan bindiga suke yi a gonakin da sanya musu haraji
  • Wani shugaban kungiyar manoma a Najeriya, Kabir Ibrahim ya yi martani kan tsarin da shugaban kasar ya kawowa manoman Arewa

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Arewa - Gwamnatin Najeriya ta fito da tsarin sanya jami'an tsaro domin hana yan bindiga kai hari a gonaki.

Sufeton yan sanda na kasa, IGP Kayode Egbetokun ya bayyana matakin da suka fara dauka a wasu yankunan Arewa.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da maganar Dan Bello, gwamnonin Arewa sun saka labule

Manoma
Gwamnati ta samar da jami'an tsaro a gonaki. Hoto: Kola Sulaimon
Asali: Getty Images

Jaridar Punch ta ruwaito cewa wata kungiyar manoma ta mika godiya ga Bola Tinubu kan kawo tsarin a daidai wannan lokacin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yan bindiga sun addabi manona

Rahotanni sun nuna cewa yan bindiga sun addabi manona a Najeriya ta inda suka kashe kimanin manoma 332.

Haka zalika ƙididdiga ta nuna cewa manoma sun biya yan bindiga harajin kudi da ya haura Naira miliyan 139 a yankin Arewa.

An saka jami'an tsaro a gonaki

Daily Post ta wallafa cewa sufeton yan sandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya tabbatar da cewa jami'an yan sanda sun fara kewayawa zuwa gonaki a Arewa Maso Gabas.

Haka zalika jami'in rundunar tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba ya ce sojoji sun fara sintiri a gonakin Arewa ta Tsakiya da ta Yamma.

Jami'an tsaro sun dauki matakin ne domin samar da cikakkiyar kariya ga manoma a lokacin damina.

Kara karanta wannan

Dattijon Arewa ya jaddadawa Tinubu matsayarsa, Yakasai ya fadi matsalar Najeriya

Kungiyar manoma ta yi godiya

Wani shugaban kungiyar manoma, Kabir Ibrahim ya ce samun jami'an tsaro a gonaki na karfafa musu gwiwa.

Sai dai duk da haka ya yi kira kan muhimmacin magance matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya baki daya.

Yan bindiga sun sace manomi a Kaduna

A wani rahoton, kun ji cewa yan bindiga sun yi awon gaba da dagacin Tunburku, Malam Ashiru Sharehu a ƙaramar hukumar Giwa ta jihar Kaduna.

Mazauna garin sun bayyana cewa maharan sun tafi da basaraken a lokacin da ya kamo hanyar dawowa gida daga gonarsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng