'Yan Ta'adda 44 Sun Ji Wuta, Sun Miƙa Wuya Yayin da Sojoji Suka Hallaka Wasu a Arewa

'Yan Ta'adda 44 Sun Ji Wuta, Sun Miƙa Wuya Yayin da Sojoji Suka Hallaka Wasu a Arewa

  • Sojoji sun yi nasarar hallaka ƴan ta'adda biyar a ƙaramar hukumar Bama ta jihar Borno, sun kwato manyan makamai
  • Rundunar ta bayyana cewa sakamakon luguden wutar da sojojin ke yi, mayaƙan Boko Haram 44 da iyalansu sun miƙa wuya
  • Sanarwar ta kara da cewa daga cikin makaman da aka kwato har da bama-bamai, bindigu, alburusai da kuma babura

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Borno - Dakarun rundunar sojojin Najeriya sun yi nasarar sheƙe ƴan ta'adda biyar a yankin ƙaramar hukumar Bama da ke jihar Borno a Arewa maso Gabas.

Bugu da ƙari, bayan tura ƴan ta'addan lahira, dakarun sojojin sun ƙwato bama-bamai, bindigun roka, babura shida da wasu kayan aiki da dama.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Babban jigo ya faɗi dalili 1 da ya kamata a tsige Tinubu da wasu gwamnoni

Dakarun sojojin Najeriya.
Sojoji sun hallaka yan ta'adda 4, wasu 44 sun mika wuya a jihar Borno Hoto: Nigerian Army
Asali: Facebook

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da rundunar sojojin kasa ta Najeriya ta fitar ranar Talata, 13 ga watan Agusta, 2024, kamar yadda Punch ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce 'yan ta'addan Boko Haram 44 da iyalansu sun mika wuya ga sojojin da aka tura kananan hukumomin Bama, Dikwa, da Gwoza na jihar Borno.

Sojoji sun kai samame sansanin ISWAP

Sanarwar ta ce:

"A ranar 12 ga Agusta, 2024, sojoji sun kai samame wani sansani da mayaƙan kungiyar ISWAP ke samun mafaka a karamar hukumar Bama ta jihar Borno.
"A samamen sojoji sun kashe ‘yan ta’adda biyar tare da kwato bama-bamai guda biyu, bindigogin roka biyu, Dane guda biyu, bom na RPG daya, AK-47 daya, harsashi 23, babura shida da magunguna iri-iri."

Boko Haram: Ƴan ta'adda sun mika wuya

Rundunar sojojin ta kara da cewa sakamakon luguden wutan da dakaru ke ci gaba da yi kan mayaƙan Boko Haram, ƴan ta'adda 44 sun miƙa wuya tare da iyalansu.

Kara karanta wannan

Dakarun sojoji sun ragargaji 'yan ta'addan Boko Haram a jihar Borno

"'Yan ta'addan Boko Haram 44 da iyalansu sun mika wuya ga sojojin da aka tura a kananan hukumomin Bama, Dikwa da Gwoza a jihar Borno," in ji sanarwar.

Yan China sun faɗa hannun masu garkuwa

A wani labarin kuma ƴan bindiga sun yi garkuwa da ƴan ƙasar China biyu da suka shigo Najeriya domin yin aiki a jihar Ogun.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, Omolola Odutola ta ce jami'an haɗin guiwa na neman ceto su.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262