Masu Zanga Zanga Sun Yi Gagarumar Nasara, Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci

Masu Zanga Zanga Sun Yi Gagarumar Nasara, Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci

  • Masu zanga-zangar tsadar rayuwa sun samu nasara a babbar kotun tarayya mai zama a Abuja a shari'ar da aka nemi dakatar da su
  • Alkalin kotun ya kori ƙarar da wasu mutane 16 suka nemi a hana ci gaba da wannan zanga-zanga da aka fara saboda ana tauye masu haƙƙi
  • Wannan dai na zuwa ne bayan kammala kwanaki 10 ana zanga-zanga kuma matasa sun sha alwashin ci gaba a watan Oktoba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta yi fatali da buƙatar hana ƴan Najeriya ci gaba da zanga-zanga mai taken #EndBadGovernance.

Kotun ta yi fatali da bukatar wanda aka nemi ta ba da umarnin wucin gadi na haramtawa kungiyoyi ci gaba da wannan zanga-zanga nan gaba a Najeriya.

Kara karanta wannan

Ranar ƙarshe: Masu zanga zanga sun sake fantsama kan tituna, ƴan sanda sun ankara

Masu zanga-zanga a Najeriya.
Tsadar rayuwa: Kotu ta yanke hukunci kan bukatar hana ci gaba da zanga-zanga a Najeriya Hoto: Contributor
Asali: Getty Images

Jaridar Leadership ta tattaro cewa Danladi Goje, Buky Abayomi, Adiza Abboda wasu mutum 13 ne suka shigar da bukatar gaban kotu ranar 12 ga watan Agusta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa aka nemi hana zanga-zanga?

Masu shigar da ƙarar sun nemi kotu ta tabbatar masu da ƴancinsu da kundin tsarin mulki ya ba su daga barazanar masu zanga-zangar.

Lauyan masu kara, Tsembelee Sorkaa, ya faɗawa kotu cewa ’yancin rayuwa, ’yancin kai, sirri da iyali, zirga-zirga, da tattalin arzikin waɗanda yake karewa na iya fuskantar barazana saboda zanga-zangar.

Kotu ta kori ƙarar nan take

Da yake yanke hukunci, mai shari'a Lifu ya bayyana cewa zanga zangar da ake ƙorafi a kanta an gama ta a makon da ya gabata.

Ya kuma ƙara da cewa lauyan masu kara ya gaza gabatar da gamsassun shaidu da za su tabbatar da cewa masu zanga-zangar za su sake komawa kan tituna.

Kara karanta wannan

Yunwa na barazana ga rayukan almajiran Kano, an roki matasa su hakura da zanga zanga

Mai shari'a Lafu ya ce:

"Na yi nazari kan wannan bukata kuma a gani na ba zai yiwu kotu ta amince ba, ƙorafin bai karɓu ba saboda haka kotu ta yi watsi da shi."

Daga nan ne kotun ta dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 29 ga Agusta, 2024, rahoton Sahara Reporters.

'Ya kamata a sauke Bola Tinubu'

Kuna da labarin tsohon mataimakin shugaban APC, Salihu Lukman ya ce zanga-zangar da aka yi kaɗai ta isa zama dalilin tsige Bola Ahmed Tinubu.

Lukman ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, 11 ga watan Agusta, 2024, sa'o'i 24 bayan kammala zanga-zangar kwanaki 10.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262