Baram Barama 7 da Shugaban Majalisar Dattawa, Akpabio Ya Yi gaban Duniya

Baram Barama 7 da Shugaban Majalisar Dattawa, Akpabio Ya Yi gaban Duniya

Abuja - Godswill Akpabio shi ne shugaban majalisar dattawan Najeriya tun watan Yunin 2023, kuma tsohon ministan Neja-Delta ne.

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Bayan rike wadannan mukamai, Godswill Akpabio ya yi kwamishina har ya zama gwamna a jiharsa ta Akwa Ibom na shekaru takwas.

Mukaman da ya rike ba su hana Sanata Godswill Akpabio sakin layi ba, an saba rahoto shi yana kauce hanya a wajen magangansa.

Akpabio
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio Hoto: Godswill Obot Akpabio
Asali: Facebook

Legit ta bibiyi lokutan da Godswill Akpabio ya jawo abin magana a dalilin kalamansa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Kudin hutun ‘yan majalisa

Watanni biyu da zamansa shugaban majalisa, Godswill Akpabio ya yi subutar baki a gaban duniya, ya ce an aikawa ‘yan majalisa kudin hutu.

Kara karanta wannan

Hauhawar farashi: Abba Gida Gida ya ji koken jama'a, gwamna ya sa labule da 'yan kasuwa

Kafin Akpabio ya ankara, ‘yan jarida sun dauki wannan magana da ya yi. Lamarin dai ya fusata irinsu Sanata Ali Ndume tun a lokacin.

2. 'Tinubu ya rabawa jihohi kudi' - Akpabio

An rahoto Akpabio yana ikirarin cewa shugaban kasa Bola Tinubu ya aikawa kowace jiha N30bn domin a magance matsalar yunwa da talauci.

Daga baya dole hadiminsa ya lashe wannan amai da ya kwaba, ba a ba wadannan kudi masu yawa da tsohon gwamnan Akwa Ibom ya fada ba.

3. Akpabio: 'A bar talaka ya sarara'

Jaridar Vanguard ta taba rahoto Akpabio yana wani bayani da wasu su ka dauke shi a matsayin izgili da talakawan da su ke cikin kunci.

Shugaban majalisar ya yi ta maimaita zancen ‘a bar talaka ya sarara’, wasu su na ganin shakiyanci ne kurum ba wai tausayin talaka ba.

4. Mafi karancin albashi

Daily Trust ta kawo labarin Sanata Akpabio ya na cewa dole duk wanda aka dauke shi aiki ko da a gida ne, sai an biya shi akalla N70, 000 a wata.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan Katsina a shirgegen muƙami, ya tura saƙo

Shugaban majalisar ya fadi haka ne ganin an sa hannu a sabon mafi karancin albashi. Daga baya bincike ya nuna ba haka dokar kasa ta ce ba.

5. Kalaman Akpabio gabanin zanga-zanga

Magangunan da ya yi daf da za a shiga zanga-zanga ya hurawa lamarin wuta, an ji ya na cewa a tafi zanga-zangar, su na nan su na cin abinci.

Akpabio ya sha sukar har daga kungiyar Amnesty Internal saboda wannan zance a mawuyacin hali, bai lura da kujerar da yake kai ba.

6. Murde zabe a lokacin PDP

A rahoton Premium Times, ana tunawa da lokacin da ‘dan siyasar ya fito fili yana fadawa duniya yadda su ka murde zabe a jihar Akwa Ibom.

An taba daukar shi a taron PDP yana bayanin ya rabawa shugaban jam’iyya N1m da nufin su ci abinci a Mr. Biggs domin samun yadda yake so.

7. Akpabio a majalisa yana Minista

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Jigon APC ya fadi abin da ya dace shugaban majalisar dattawa ya yi

Mr Akpabio yana minista aka gayyace shi majalisa bisa zargin cushen kwangilolin N500m a kasafin kudin hukumar NDDC a shekarar 2017.

Da ya je majalisar tarayyan, ministan na Neja Delta ya nemi tona asirin kowa, a karshe sai dai aka rika rokonsa ya yi shiru ya rufe bakinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng