An Yi Wa Gwamnatin Tinubu Bakin Tambari; Amnesty Int'l Ta Soki Kutsen Jami'an Tsaro a Ofishin NLC

An Yi Wa Gwamnatin Tinubu Bakin Tambari; Amnesty Int'l Ta Soki Kutsen Jami'an Tsaro a Ofishin NLC

  • Yayin da aka wayi gari da labarin samamen da jami'an tsaro su ka kai babban ofishin kungiyar kwadago ta NLC, kungiyoyi sun fara raddi
  • Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta bayyana samamen a matsayin karan tsaye ga hakkin 'yan kasar nan
  • Shugaban kungiyar na Najeriya, Sanusi Isa ya bayyana cewa an kai samamen ne ba komai ba sai domin tsorata kungiyoyin kwadago

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Kungiyar kare hakkin dan Adam ta duniya, Amnesty International ta caccaki hukumomin Najeriya bisa samamen da su ka kai ofishin kungiyar kwadago ta kasa.

A ranar Alhamis ne aka tashi da labarin jami'an tsaro na fararen kaya (DSS) sun kutsa babban ofishin kungiyar kwadago ta NLC da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Hauhawar farashi: Abba Gida Gida ya ji koken jama'a, gwamna ya sa labule da 'yan kasuwa

Nigeria Labour Congress HQ
Amnesty Int'l ta yi tir da kutsen ofishin NLC da jami'an DSS su ka yi Hoto: Nigeria Labour Congress HQ
Asali: Facebook

Jaridar Punch ta wallafa cewa a sanarwar da Amnesty Int'l ta fitar yau Alhamis, ta bayyana zargin jami'an sun dauki matakin domin cusa tsoro a zukatan jagororin kwadago a kasar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ana zargin DSS ta kai samamen ne bisa zargin kungiyar kwadagon na da hannu wajen kitsa zanga-zangar adawa da manufofin gwamnatin Bola Tinubu.

"Akwai barazana ga NLC," Amnesty Int'l

Kungiyar hakkin bil adama ta Amnesty Int'l ta bayyana damuwa a kan tsaron rayukan shugabannin kungiyar kwadago ta NLC bayan jami'an DSS sun kutsa ofishinsu.

Sanusi Isa, wanda shi ne shugaban kungiyar na Najeriya ya bayyana kaduwa a kan yadda jami'an su ka yiwa doka karan tsaye wajen kai samamen.

Channels Television ta tattaro cewa kungiyar na zargin samamen wani shiryayyen hari ne a kan kwadago a kasar nan.

NLC ta yi martani kan kutsen DSS

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Majalisar matasan Arewa ta yi fatali da neman dauke cibiyar NCC daga Kano

A baya mun ruwaito cewa kungiyar kwadago ta kasa (NLC) ta yi Allah wadai da yadda jami'an 'yan sanda da na DSS su ka tirsasa shiga ofishinta a wani yunkuri na neman muhimman bayanai.

Sakataren kungiyar, Benson Upah ya ce wannan abin kunya ne matuka, ganin yadda ko a zamanin soja ba a yiwa hakkinta karen tsaye makamancin wanda aka gani a daren Laraba ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.