Hauhawar Farashi: Abba Gida Gida Ya Ji Koken Jama'a, Gwamna Ya Sa Labule da 'Yan Kasuwa

Hauhawar Farashi: Abba Gida Gida Ya Ji Koken Jama'a, Gwamna Ya Sa Labule da 'Yan Kasuwa

  • Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya zauna da 'yan kasuwa domin lalubo hanyar magance hauhawar farashi
  • Tun bayan fara zanga-zangar tsadar rayuka masu shaguna su ka kara farashin kayan masarufi, wanda su ka dora laifin a kan manyan yan kasuwa
  • A zaman da aka yi ranar Laraba, an tattauna muhimman batutuwa da su ka jibinci sauko da farashin kayan da ci gaban tsaro a jihar

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Gwamnatin Kano ta gayyaci kungiyar 'yan kasuwar jihar domin gano dalilin tsadar kayayyaki tun bayan fara zanga-zanga a ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

Bayan zanga zanga, Abba ya dauko muhimman ayyuka 7 domin farfaɗo da Kano

Mazauna Kano sun koka bisa yadda aka samu tsadar kayayyaki, yayin da ake rasa wasu daga cikin kayan masarufi a shagunan cikin unguwanni.

Abba Kabir Yusuf
Abba Gida-Gida ya gana da 'yan kasuwa a kan hauhawar farashi Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa jama'a na shan wahala sosai, saboda haka ya kamata 'yan kasuwa su daidaita farashinsu,

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan ya nusar da su a kan su da su ji tsoron Allah, su sassautawa jama'ar Kano ta hanyar rage farashi yadda ya kamata.

Abba Gida-Gida ya nemi hadin 'yan kasuwa

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hadin kan 'yan kasuwa wajen tsaftace kasuwanni a kokarin gwamnatinsa na tsaftace jihar Kano.

Gwamnan ya yi alkawarin sanya fitilun kan titi a kasuwar kwari domin karfafa harkar tsaro kamar yadda daraktan yada labaransa, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Majalisar matasan Arewa ta yi fatali da neman dauke cibiyar NCC daga Kano

'Yan kasuwa da gwamnatin Kano sun cimma matsayar ci gaba da hadin kai domin magance matsalolin da su ka addabi jihar.

Kano: Abba Gida-Gida zai yi manyan ayyuka

A wani labarin kun ji cewa gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan 2.67 domin gudanar da manyan ayyuka a jihar, ciki har da samar da matsuguni ga ma'aikatar sufuri.

An amince da fitar da makudan kudin a zaman majalisar zartarwa da ya gudana ranar Talata, inda aka fitar da ₦164,949,693.46 domin sake gina shataletalen gidan gwamnati.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.