Ana Daga Tutar Rasha, Amurka da Birtaniya Sun Fadi Matsaya kan Manufofin Tinubu

Ana Daga Tutar Rasha, Amurka da Birtaniya Sun Fadi Matsaya kan Manufofin Tinubu

  • Yayin da ake cigaba da zanga-zanga a Najeriya, gwamnatocin Amurka da Burtaniya sun yi martani kan halin da ake ciki
  • Kasashen biyu sun tura sakon jaje ga wadanda suka rasa rayukansu yayin zanga-zangar da aka kwashe kwanaki bakwai ana yi
  • Wannan martani na kasashen na zuwa ne yayin da ake zanga-zanga a Najeriya kan halin matsi da kuma tabarbarewar tsaro

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Gwamnatocin Amurka da Burtaniya sun yi magana kan zanga-zanga da ake yi a Najeriya.

Duka kasashen biyu sun yaba da tsare-tsaren Bola Tinubu musamman a fannin tattalin arziki.

Burtaniya da Amurka sun tsoma baki kan zanga-zanga a Najeriya
Kasashen Amurka da Burtaniya sun yi magana kan zanga-zanga. Hoto: @JoeBiden, @DOlusegun, @Keir_Starmer.
Source: Twitter

Martanin Amurka da Burtaniya kan zanga-zanga

Wannan na kunshe a cikin sanarwa da kasashen suka fitar mabambanta a yau Laraba 7 ga watan Agustan 2024, cewar The Nation.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: A karshe, Ganduje ya yi magana, ya tura sako ga 'yan Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kasashen sun bukaci shugaban ya cigaba da neman hanyar tattaunawa da masu zanga-zangar domin shawo kan matsalar, Punch ta tattaro.

Jakadan Burtaniya a Najeriya, Richard Montgomery da na Amurka, Richard Mills sun yabawa jami'an tsaro yadda suka gudanar da zanga-zangar.

Zanga-zanga: Kasashen biyu sun yabawa tsare-tsaren Tinubu

Mills a bangarensa ya jajantawa iyalan wadanda suka rasu ko tafka asara ta kowane hali yayin da ake zanga-zangar.

Ya ce tsare-tsaren Tinubu sun zama dole kuma Amurka tana goyon baya domin tabbatar da bunkasar tattalin arziki a Najeriya.

Montgomery shi kuma ya yabawa jami'an tsaro kan yadda ba su yi amfani da karfi ba kan matasa da ke zanga-zanga.

Ya ce sun san yadda Gwamnatin Najeriya ta himmatu wurin tabbatar da an gudanar da zanga-zangar cikin lumana.

Dalilin Tinubu na kin dawo da tallafi

A wani labarin, kun ji cewa Ministan kudi a Najeriya, Wale Edun ya yi magana kan dalilin da ya sa Bola Tinubu ba zai dawo da tallafin mai ba.

Kara karanta wannan

"Ku amshi tayin gwamnati," Sarki ya lallashi masu zanga zanga

Wale Edun ya ce babu kason tallafin mai a cikin kasafin da Tinubu ya mika a Majalisar Tarayya na wannan shekara ta 2024.

Martanin na zuwa ne yayin da masu zanga-zanga ke bukatar shugaban ya dawo da tallafin man fetur kamar yadda ya cire.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.