Ana Daga Tutar Rasha, Amurka da Birtaniya Sun Fadi Matsaya kan Manufofin Tinubu

Ana Daga Tutar Rasha, Amurka da Birtaniya Sun Fadi Matsaya kan Manufofin Tinubu

  • Yayin da ake cigaba da zanga-zanga a Najeriya, gwamnatocin Amurka da Burtaniya sun yi martani kan halin da ake ciki
  • Kasashen biyu sun tura sakon jaje ga wadanda suka rasa rayukansu yayin zanga-zangar da aka kwashe kwanaki bakwai ana yi
  • Wannan martani na kasashen na zuwa ne yayin da ake zanga-zanga a Najeriya kan halin matsi da kuma tabarbarewar tsaro

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Gwamnatocin Amurka da Burtaniya sun yi magana kan zanga-zanga da ake yi a Najeriya.

Duka kasashen biyu sun yaba da tsare-tsaren Bola Tinubu musamman a fannin tattalin arziki.

Burtaniya da Amurka sun tsoma baki kan zanga-zanga a Najeriya
Kasashen Amurka da Burtaniya sun yi magana kan zanga-zanga. Hoto: @JoeBiden, @DOlusegun, @Keir_Starmer.
Asali: Twitter

Martanin Amurka da Burtaniya kan zanga-zanga

Kara karanta wannan

Zanga zanga: A karshe, Ganduje ya yi magana, ya tura sako ga 'yan Najeriya

Wannan na kunshe a cikin sanarwa da kasashen suka fitar mabambanta a yau Laraba 7 ga watan Agustan 2024, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kasashen sun bukaci shugaban ya cigaba da neman hanyar tattaunawa da masu zanga-zangar domin shawo kan matsalar, Punch ta tattaro.

Jakadan Burtaniya a Najeriya, Richard Montgomery da na Amurka, Richard Mills sun yabawa jami'an tsaro yadda suka gudanar da zanga-zangar.

Zanga-zanga: Kasashen biyu sun yabawa tsare-tsaren Tinubu

Mills a bangarensa ya jajantawa iyalan wadanda suka rasu ko tafka asara ta kowane hali yayin da ake zanga-zangar.

Ya ce tsare-tsaren Tinubu sun zama dole kuma Amurka tana goyon baya domin tabbatar da bunkasar tattalin arziki a Najeriya.

Montgomery shi kuma ya yabawa jami'an tsaro kan yadda ba su yi amfani da karfi ba kan matasa da ke zanga-zanga.

Ya ce sun san yadda Gwamnatin Najeriya ta himmatu wurin tabbatar da an gudanar da zanga-zangar cikin lumana.

Kara karanta wannan

"Ku amshi tayin gwamnati," Sarki ya lallashi masu zanga zanga

Dalilin Tinubu na kin dawo da tallafi

A wani labarin, kun ji cewa Ministan kudi a Najeriya, Wale Edun ya yi magana kan dalilin da ya sa Bola Tinubu ba zai dawo da tallafin mai ba.

Wale Edun ya ce babu kason tallafin mai a cikin kasafin da Tinubu ya mika a Majalisar Tarayya na wannan shekara ta 2024.

Martanin na zuwa ne yayin da masu zanga-zanga ke bukatar shugaban ya dawo da tallafin man fetur kamar yadda ya cire.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.