Zanga Zanga: Sanusi II Ya Fadi Masu Laifi kan Barnar da Aka Yi a Kano, Ya Yi Addu’a

Zanga Zanga: Sanusi II Ya Fadi Masu Laifi kan Barnar da Aka Yi a Kano, Ya Yi Addu’a

  • Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya koka kan rawar da jami'an tsaro suka taka kafin faruwar zanga-zanga a jihar
  • Sarkin ya ce tun kafin faruwar hakan an rubutawa jami'an tsaro domin daukar mataki amma suka yi sakaci har aka yi barna
  • Sanusi II ya koka kan yadda aka lalata dukiyoyi da kuma rasa rayukan al'umma inda ya ce barnar da aka yi shiryawa aka yi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya yi magana kan zanga-zanga da ake cigaba da yi musamman a jihar.

Sarkin Kano ya bayyana cewa rashin daukar matakan da ya dace da sakacin jam'ian tsaro ne ya jawo rasa rayuka da dukiyoyi.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: A karshe, Ganduje ya yi magana, ya tura sako ga 'yan Najeriya

Sarki Sanusi II ya dauka alhakin barnan da aka yi a Kano kan makiyanta
Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya nuna damuwa kan barnar da aka yi a Kano yayin zanga-zanga. Hoto: @masarautarkano.
Asali: Twitter

Muhammadu Sanusi II ya magantu kan zanga-zanga

Sanusi II ya bayyana haka ne yayin ziyara a cibiyar NCC Digitar Park da sauran wurare da aka farfasa a jihar, cewa Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Basaraken ya ce an sanar da jam'ian tsaro kan lamarin amma ba su dauki matakin da ya dace ba har aka kaddamar da harin kan dukiyoyi.

Ya ce duk wadanda suka yi barna a jihar makiya Kano ne kuma daman an riga an shirya hakan duk wanda ya lura zai gane.

Zanga-zanga: Sanusi II ya ce akwai hannun makiya

"Abin da muke fada ne, duk mai hanu a wannan lamari makiyin Kano ne da mutanenta, abin da ya faru a Kano shiryawa aka yi."
"Ana son rusa jihar Kano amma muna addu'ar Allah ya hana su samun nasara muna rokon Ubangiji ya mayar da mafi alheri."

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna a Arewa na daukar nauyin zanga zanga? an gano gaskiya

"Kafin faruwar haka an fadawa jam'ian tsaro a rubuce madadin kare faruwar hakan amma suka bari aka aikata barna, duk mai hannu a ciki zai ga sakamakonsa."

- Muhammadu Sanusi II

Sarkin daga bisani ya yi addu'ar Allah ya ba gwamnati damar dawo da abin da jihar ta rasa inda ya ce matasa suna bukatar addu'a sosai.

Sanusi II ya gargadi matasa kan zanga-zanga

Kun ji cewa Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya yi magan mai kama hankali kan shirin gudanar da zanga-zanga a Najeriya.

Sanusi II ya shawarci matasa da su guji shiga lamarin zanga-zangar da aka shirya fita gobe Alhamis 1 ga watan Agustan 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.