An Samu Sabani Tsakanin 'Yan Sanda da Rundunar Sojoji a kan Harbin 'Yan Zanga Zanga

An Samu Sabani Tsakanin 'Yan Sanda da Rundunar Sojoji a kan Harbin 'Yan Zanga Zanga

  • Bayan babban Sufeton 'yan sandan kasar nan, Kayode Egbetokun ya karyata rahotannin cewa jami'ansu sun harbi masu zanga-zanga
  • Rundunar sojojin kasar nan ta tabbatar da cewa jami'an tsaro sun bude wuta a kan jama'a masu zanga-zangar adawa da manufofin gwamnati
  • Daraktan yada labaran rundunar, Onyeama Nwachukwu ya bayyana cewa harbin ne ma ya yi sanadin rasuwar matashi mai shekaru 16 a Zariya

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - An samu bambancin furuci tsakanin hukumomin tsaron kasar nan a kan harba bindiga yayin zanga-zangar lumana da matasan kasar nan ke gudanarwar.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Majalisar matasan Arewa ta yi fatali da neman dauke cibiyar NCC daga Kano

Tun a ranar Alhamis da aka fara gudanar da zanga-zangar aka ji harbin bindiga a wasu jihohin kasar nan kamar Kano da Legas.

Sojoji
Rundunar soja ta tabbatar da harba binga yayin zanga-zanga Hoto: HQ Nigerian Army
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa amma babban sufeton yan sanda, Kayode Egbetokun ya fito bainar jama'a ya na cewa babu jami'insu da ya harbi matasan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun karyata Sufetan yan sanda

Gabanin rundunar sojojin kasar nan ta bayyana cewa an yi harbi har ya jawo asarar rai a Zariya, an samu rahotannin wuraren da aka ji harbe-harbe.

Punch News ta wallafa cewa rundunar ta tabbatar da cewa jami'inta ne ya halaka matashi mai shekaru 16 a Samaru.

Wuraren da aka ji harbe-harbe lokacin zanga-zanga

An ji karar bindiga a jihar Neja inda aka yi zargin harbin mutum shida, sai kuma a Kubwa, Abuja da fargabar kashe matashi guda.

Kara karanta wannan

Yadda aka kashe budurwa mai shirin zama amarya da wasu matasa a zanga zanga a Arewa

Rahotannin harbe-harbe sun sun bulla a Bauchi, Kano, Jigawa, Katsina da Borno har da fargabar rasa rayuka.

Kisan matashi: Rundunar soja za ta yi hukunci

A baya kun ji cewa rundunar sojojin kasar nan ta bayyana takaici da alhini bisa yadda jami'inta ya halaka matashi mai shekaru 16 a Samaru, Kaduna.

Daraktan yada labaran rundunar, Manjo janar Onyeama Nwachukwu ya tabbatar da kisan, sannan ya ce an kama bankin da ake zargi domin ladabtarwa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.