Masu Zanga Zanga Sun Harzuka, Za a Gudanar da Makokin Wadanda Aka Kashe

Masu Zanga Zanga Sun Harzuka, Za a Gudanar da Makokin Wadanda Aka Kashe

  • Bayan an samu mutuwar wasu daga cikin masu zanga-zanga a fadin Najeriya, jagororin tattakin sun sanya ranakun makoki
  • Wannan na kunshe cikin sanarwar da Hassan Soweto, Ayoyinka Oni da Adegboyega Adeniji su ka sanyawa hannu
  • An samu akasi bayan wasu daga cikin masu zanga-zangar sun rasa rayukansu a lokacin da jami'an tsaro su ka bude masu wuta

. A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Legas - Masu zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya sun koka bisa yadda jami'an tsaro su ka kashe wasu daga cikinsu.

An samu rahoton kisan wasu daga cikin masu zanga-zanga da matasa 'yan ba ruwana a jihohin Kano, Kaduna da Katsina.

Kara karanta wannan

Yadda aka kashe budurwa mai shirin zama amarya da wasu matasa a zanga zanga a Arewa

Legas
Za a yi makokin masu zanga-zanga da yan sanda su ka kashe Hoto: NurPhoto
Asali: Getty Images

Jaridar Premium Times ta wallafa cewa Hassan Soweto, Ayoyinka Oni da Adegboyega Adeniji ne su ka sanya hannu a kan sanarwar makokin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sun ce dole ne su nuna alhini a kan yadda jami'an tsaro su ka rika kashe su saboda sun fito neman a saukaka masu halin da kasa ke ciki.

Za a yi makokin kwanaki 3

Mutanen da su ke jagorantar zanga-zanga a jihar Legas sun fitar da tsarin yadda za a yi makokin mutanen da jami'an tsaro su ka kashe a kasar nan.

Jaridar Guardian ta wallafa cewa masu zanga-zangar sun dauki matakin nuna alhininsu a fili tun da gwamnatin Legas da 'yan sanda sun ki ba su kariya.

Za a gudanar da makokin daga Laraba zuwa Juma'a ta hanyar gudanar da taro ta shafin X, sannan a ɗora da tattakin rike kyandir a jihar.

Kara karanta wannan

"An yi abin kunya", Rundunar soja ta yi tir da masu sata a wuraren ibada ana zanga zanga

An shiga makoki a Kaduna

A baya mun ruwaito yadda wani jami'in rundunar sojojin kasar nan ya jefa mazauna yankin Samaru a cikin takaici bayan ya harbe wani matashi.

Bayanai sun nuna cewa sojojin sun bude wuta a lokacin da su ka shiga Unguwar Pawa wanda ya sa kowa shiga, amma wani soja ya harbi kofar gidan yaron har ya rasu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.