Tsaro: Gwamnati Ta Fitar da Makudai a Watanni 6, An Kashe Naira Tiriliyan 1

Tsaro: Gwamnati Ta Fitar da Makudai a Watanni 6, An Kashe Naira Tiriliyan 1

  • Rashin tsaro da ya zama karfen kafa a kasar nan ya na ci gaba da daukar hankali, yayin da aka gano makudan kudin da gwamnati ta kashe
  • Alkaluman da aka tattaro sun nuna yadda gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta fitar da Naira Tiriliyan 1 domin yakar ta'addanci
  • An gano cewa an fitar da kudin ne a cikin watannin shidan farkon shekarar 2024; daga Janairu zuwa Yuni

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Yayin da rashin tsaro ya ke kamari a Najeriya, an gano yadda gwamnatin tarayya ta fitar da kudi masu nauyi domin yakar ta'addanci.

Kara karanta wannan

Bayan zanga zanga, Abba ya dauko muhimman ayyuka 7 domin farfaɗo da Kano

Daga watan Janairu zuwa Yuni, 2024, gwamnati ta fitar da N1.03tr domin yaki da ta'addanci a sassan Najeriya.

Tinubu
Gwamnati ta fitar da sama da N1trn a kan rashin tsaro Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Jaridar Punch ta tattaro cewa kudin da aka fitar ya kai 42.80% na kasafin Naira Tiriliyan 2.41, wanda ke nufin yanzu Naira Tiriliyan 1.38 ya rage a kasafin da aka warewa bangaren tsaro.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Duk da kasafin tsaro, Ana kashe jama'a

Alkaluman da aka tattaro sun nuna yadda ake samun karuwar hare-haren 'yan ta'adda duk da makudan kudin da gwamnati ta fitar ga bangaren.

An gano cewa zuwa yanzu, an 'yan kashe mutane 5,801 a hare-hare daban-daban, kuma an sace mutane 4,348 a watannin bakwai na farkon 2024.

Wuraren da rashin tsaro ya fi kamari

An kashe mutane da sace wadansu a kananan hukumomin kasar nan 574 daga cikin 774 da ake da su a fadin Najeriya.

Kara karanta wannan

Kano: Gwamnatin Abba Gida Gida ta amince da fitar da N2.67bn domin manyan ayyuka

Arewa maso Gabas ce ta fi fuskantar matsala inda aka kashe mutane 2,223 a hare-hare da miyagu su ka kai kananan hukumomi 88 a yankin.

Gwamnati ta tsaurara tsaro a Kano

A wani labarin kun ji cewa gwamnatin Kano ta bayyana cewa tuni ta tsaurara tsaro a sassan jihar bayan sassauta dokar takaita zirga-zirga da aka sanya biyo bayan rikicin zanga-zanga.

Kwamishinan 'yan sandan Kano, Salman Dogo ne ya bayyana haka, inda ya nemi hadin kan mazauna jihar domin tabbatar da wanzuwar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.