Masu Zanga Zanga sun Ƙwace Motar Yaƙin Ƴan Sanda a Kaduna? Gaskiya ta Fito

Masu Zanga Zanga sun Ƙwace Motar Yaƙin Ƴan Sanda a Kaduna? Gaskiya ta Fito

  • Rundunar 'yan sanda ta yi martani kan rahotannin da ake yadawa a shafukan intanet na cewa masu zanga-zanga sun kwace motar 'yan sanda
  • Wani faifan bidiyo da ya yadu a shafukan sada zumunta ya nuna lokacin da masu zanga zanga suka yi rade-rade kan motar 'yan sanda a Kaduna
  • Sai dai kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya ce wannan rahoto ko bidiyo da ake yadawa ba gaskiya bane, babu motarsu da aka kwace

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Rundunar 'yan sandan Najeriya ta yi magana kan wani bidiyo da ya yadu a soshiyal midiya inda aka ga masu zanga-zanga sun yi dafifi saman wata motar yakin 'yan sanda.

Kara karanta wannan

Legas: 'Yan daba sun kai mamaya kusa da ofishin gwamna, an tarwatsa masu zanga zanga

Mafi akasarin wadanda ke wallafa bidiyon, sun shaida cewa masu zanga-zangar sun kwace motar yakin ne daga hannun jami'an 'yan sandan a jihar Kaduna.

Rundunar 'yan sanda ta yi magana kan zargin kwace motarta a Kaduna
Kaduna: 'Yan sanda sun karyata kwace motarta a Kaduna. Hoto: @Princemoye1
Asali: Twitter

Sai dai, a wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan na kasa, Prince Olumuyiwa Adejobi ya fitar a shafinsa na X, an gano akasin ikirarin mutane.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bidiyo: Matasa a kan motar 'yan sanda

Fitaccen mawakin Kudu, Charly Boy ya wallafa a shafinsa na X a jiya Litinin cewa masu zanga-zanga sun kwace motar 'yan sanda mai sulke.

Mawakin ya nuna damuwarsa kan yadda masu zanga-zangar suka yi dare-dare a kan motar yayin da yake nuna damuwarsa kan halin da kasar ke ciki.

Kalli bidiyon a kasa:

Masu zanga-zanga sun kwace motar 'yan sanda?

Sai dai a martanin da Prince Olumuyiwa Adejobi ya yi, ya ce ba a kwace motar sulke ta ‘yan sanda ba, sabanin faifan bidiyo da ake yadawa a yanar gizo.

Kara karanta wannan

Masu zanga zanga na daga tutar Rasha a Kaduna, an fara awon gaba da kayan jama'a

Sanarwar kakakin rundunar ya ce masu zanga-zangar sun dare kan motar ne a lokacin da take kokarin barin wajen domin kai agaji a wani wuri na daban.

"Motar ta dawo sansanin da take, kuma tun kafin ta karasa masu zanga-zangar suka sauka tare da ranta a na kare. Babu wata motar 'yan sanda da masu zanga-zanga suka kwace a Kaduna."

- Inji kakakin rundunar.

Prince Olumuyiwa Adejobi ya yi kira ga 'yan Najeriya da su yi watsi da wannan rahoto ko bidiyo da ake yadawa na cewa masu zanga-zanga sun kwace motar 'yan sanda a Kaduna.

Kaduna: Matasa na daga tutar Rasha

A wani labarin, mun ruwaito cewa zanga-zanga ta fara tsananta a jihar Kaduna yayin da aka ga wasu matasa suna daga tutar kasar Rasha duk a cikin adawa da tsadar rayuwa.

Wani faifan bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta ya nuna lokacin da masu zanga-zangar ke balle kadarorin gwamnati suna awon gaba da su a yankin NEPA da ke jihar.

Kara karanta wannan

Zargin kashe masu zanga zanga: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamitin bincikar jami'an tsaro

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.