Zanga-Zanga: Tinubu Ya Fadi Yadda Za a Ci Gajiyar Shinkafar N40,000, Ya Saka Ka’ida

Zanga-Zanga: Tinubu Ya Fadi Yadda Za a Ci Gajiyar Shinkafar N40,000, Ya Saka Ka’ida

  • Yayin da ake cigaba da zanga-zanga a Najeriya, Gwamnatin Tarayya ta shirya fara siyar da shinkafar N40,000 a kasar
  • Gwamnatin ta ce ma'aikatan gwamnati ne za su ci gajiyar tallafin na shinkafa mai rahusa domin rage radadi ga al'umma
  • Ma'aikatar ayyuka na musamman ita ta bayyana haka a cikin wata sanarwa inda ta ce za a tabbatar da adalci a rabon shinkafar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Gwamnatin Tarayya ta kammala shirin fara siyar da shinkafa mai nauyin 50kg kan N40,000 kacal a Najeriya.

Gwamnatin ta dauki wannan matakin ne domin ragewa 'yan kasar halin kunci da suke ciki na mawuyacin hali a Najeriya.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Gwamnatin Kano ta ɗauki matakai 6, ta yi magana kan ɗaga tutar Rasha

Tinubu zai fara siyar da shinkafar N40,000 ga ma'aikata
Gwamnatin Bola Tinubu ta fadi yadda za a siyar da shinkafar N40,000. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Shinkafar N40,000: Tinubu ya fadi tsare-tsaren tallafin

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Ma'aikatar ayyuka na musamman ta fitar, kamar yadda Punch ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce ma'aikatan gwamnati ne kadai za su ci gajiyar shinkafar inda aka ba su sharudan cike ka'ida domin samun tallafin.

Ma'aikatar ta ce biyan kudi da kuma rarraba shinkafar za a gudanar da su cikin tsari domin tabbatar da yin adalci, cewar TheCable.

Yadda za a ci gajiyar shinkafar N40,000

"A kokarin Gwamnatin Tarayya na ragewa al'umma radadin da ake ciki, gwamnati ta shirya fara siyar da shinkafa ga ma'aikata."
"Ina mai sanar da ku cewa za a siyar da shinkafa mai nauyin 50kg kan N40,000 ga ma'aikatan da suke da bukata a Abuja."
"Duk masu sha'awa za su cike bayanansu ta yanar gizo kamar haka: https://www.ohcsf.gov.ng domin samun damar cin gajiyar."

Kara karanta wannan

Kaduna, Zariya: Gwamna ya sanya dokar hana fita ta awa 24, an ba jami'an tsaro umarni

- Cewar sanarwar

'Yan Kano sun koka kan zanga-zanga

Kun ji cewa mazauna Kano da dama sun fara kokawa kan yadda aka fara rasa kayan masarufi dalilin zanga-zanga ada ake yi.

Jama'a da dama suka ce kulle kasuwanni da ake cigaba da yi ya tilasta karewar kayan masarufi a shaguna da yawa.

Hakan bai rasa nasaba da cigaba da zanga-zanga da ake yi da kasuwanni suka kasance a kulle na tsawon kwanaki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.