Legas: 'Yan Daba Sun Kai Mamaya kusa da Ofishin Gwamna, An Tarwatsa Masu Zanga Zanga

Legas: 'Yan Daba Sun Kai Mamaya kusa da Ofishin Gwamna, An Tarwatsa Masu Zanga Zanga

  • Wasu masu zanga-zanga a kusa da ofishin gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu da ke kan titin Alausa sun ranta a na kare
  • An ruwaito cewa masu zanga-zangar sun tarwatse tare da gudun ceton rai bayan da 'yan daba suka farmake su da makamai
  • Wata majiya ta ce jami'an tsaron da aka jibe a kusa da wajen sun juya baya yayin da 'yan daban ke fatattakar masu zanga-zangar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Legas - 'Yan daba sun fatattaki wasu daga cikin masu gudanar da zanga-zanga a kan titunan Alausa, hedikwatar gwamnati a jihar Legas.

An ce ofishin Gwamna Babajide Sanwo-Olu yana a Aluasa, inda masu zanga-zangar suka yi dafifi bayan kin zuwa filin shakatawa na Freedom dake Ojota, inda kotu ta amince da gudanar da zanga-zangar a Legas.

Kara karanta wannan

Masu zanga zanga na daga tutar Rasha a Kaduna, an fara awon gaba da kayan jama'a

'Yan daba sun tarwatsa masu zanga-zanga a kusa da ofishin gwamnan Legas
Legas: Masu zanga-zanga sun ranta a na kare bayan 'yan daba sun farmake su. Hoto: PIUS UTOMI EKPEI/AFP
Asali: Getty Images

Sai dai kuma, da misalin karfe 12:00 na rana, ‘yan daba sun farmaki masu zanga-zangar da sanduna, adduna da makamai daban-daban inji rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Yan daba sun farmaki masu zanga-zanga

Ganin irin wahalar da za su iya sha, ya tilasta masu zanga-zangar ranta a na kare idan suka tarwatse kowa ya kama gabansa yayin da 'yan daban suka rika bin bayansu

An ruwaito cewa jami'an tsaron da aka girke a wajen sun yi biris kamar ba su ga abin da ke faruwa ba yayin da masu zanga-zangar ke gudun ceton rai.

Wannan dai na zuwa ne awanni 24 bayan wasu 'yan daba sun fatattaki masu zanga-zanga daga filin shakatawa na Freedom jim kadan bayan jawabin Shugaba Bola Tinubu.

Tinubu ya aika sako ga 'yan Najeriya

A ranar Lahadi ne Legit Hausa ta ruwaito cewa Bola Tinubu ya yi kira ga matasa a fadin kasar da su kawo karshen zanga-zangar yayin da gwamnatinsa ta dauki matakan gyara.

Kara karanta wannan

Jami'an tsaro sun cafke masu zanga-zangar lumana a Abuja

Shugaban kasar wanda ya ce zanga-zangar da ake yi ta rikide zuwa tashin hankali ya ce ba zai zura ido wasu 'yan siyasa su tarwatsa kasar ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.