An Gano Abin da Ya Faru da Masu Zanga Zanga Suka Nufi Gidan Buhari da Sarkin Daura

An Gano Abin da Ya Faru da Masu Zanga Zanga Suka Nufi Gidan Buhari da Sarkin Daura

  • Yayin da aka yada jita-jitar cewa wasu masu zanga-zanga sun kai hari gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, an gano gaskiya
  • Masarautar Daura ta yi martani kan lamarin inda ta musanta taba gidan Buhari ko kuma na Sarkin Daura a jihar Katsina
  • Masarautar ta ce babu wanda ya taba gidajen biyu hasalima wucewa kawai suka yi yayin da suke zanga-zangar ta su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Katsina - Masarautar Daura ta yi magana bayan jita-jitar cewa masu zanga-zanga sun dira gidan Sarkin garin da na Muuhammadu Buhari.

An ruwaito cewa wasu masu zanga-zanga sun yi dafifi a gidan tsohon shugaban kasa da kuma Sarkin Daura a jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Bayan Legas: Matasan wata jihar Kudu sun ji kiran Tinubu, sun dakatar da zanga zanga

Masarautar Daura ta musanta hari a gidan Buhari da na Sarki
Masarautar Daura ta karyata jita-jitar cewa masu zanga-zanga sun kai hari gidan Buhari da na Sarki. Hoto: Muhammadu Buhari.
Asali: Facebook

Zanga-zanga: An karyata kai hari gidan Buhari

Kakakin Sarkin Daura, Usman Ibrahim Yaro ya musanta cewa matasan sun taba gidajen Buhari da na sarkin, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yaro ya ce masu zanga-zangar ba su yi ko kusa da gidajen ba sun wuce ne kawai ta wurin yayin da suke nuna damuwa kan halin kunci.

Ya ce duk da matasan sun farfasa allunan hoton 'yan siyasa a Daura amma ba su taba na kofar gidan Buhari da na Sarkin ba.

Masarautar Daura ta yi magana kan zanga-zanga

"Masu zanga-zanga ba su taba gidan Buhari da na Sarkin Daura ba labarin da ake yadawa karya ne kawai."
"Ba a samu matsala a zanga-zanga da aka yi ba a Daura, mutane yawanci sun yi ta bukukuwan aure yayin dokar kulle da aka yi."

Kara karanta wannan

Bidiyo: Jawabin Tinubu ya fara tasiri, matasa sun janye zanga zanga a birnin Legas

- Usman Ibrahim Yaro

Yaro ya ce faifan bidiyon da ake yadawa ba gaskiya ba ne saboda an yi zanga-zanga a Daura amma babu tashin hankali.

Tinubu ya magantu kan tallafin mai

Kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya yi magana kan dawo da tallafin man fetur da ya jefa al'umma cikin kunci a Najeriya.

Shugaban ya ce cire tallafin ya zama dole duk da ya san halin kunci da hakan ya jefa 'yan Najeriya a ciki na tsawon lokaci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.