Sanata Mai Ci Na Daukar Nauyin Masu Zanga Zanga? Gaskiya Ta Fito

Sanata Mai Ci Na Daukar Nauyin Masu Zanga Zanga? Gaskiya Ta Fito

  • Yayin da ake zargin sanata mai ci da daukar nauyin masu zanga-zanga, Sanata Ireti Kingibe ta yi martani kan lamarin
  • Sanata Kingibe ta musanta karairayin da ake yi inda ta ce tsohon bidiyo aka dauko domin bata musu suna yayin zanga-zanga
  • Hakan ya biyo bayan zargin da ake yadawa cewa an gano sanatan tana raba abinci ga masu zanga-zanga a birnin Abuja

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Sanata Ireti Kingibe ta yi martani kan zargin da ake yi mata na daukar nauyin masu zanga-zanga a birnin Abuja.

Kingibe ta musanta cewa tana da hannu a lamarin wanda Ministan Abuja, Nyesom Wike ya yi zargi yayin da ake zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Sarki Sanusi ya bayyana mummunar illar da zanga zanga ta jawo a Kano da Arewa

Sanata ta yi magana kan zargin ɗaukar nauyin masu zanga-zanga
Sanata Ireti Kingibe ta musanta hannu a daukar nauyin masu zanga-zanga. Hoto: @ireti_kingibe, @GovWike.
Asali: Twitter

Zanga-zanga: Sanata ta nuna damuwa kan zarginta

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ta fitar ta bakin hadiminta a bangaren sadarwa, Kennedy Mbele, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanatar ta ce ta ji ba dadi kan wadannan karairayi da aka danganta da ita yayin da ake cigaba da zanga-zanga a kasar.

Ta ce bidiyon da ake yadawa ya kai makwanni shida inda ake wata ganawa na masu ruwa da tsaki na jam'iyyar LP.

Sanata ta fadi gaskiya kan masu zanga-zanga

"Na kadu da samun labarin karairayi cewa ni nake daukar nauyin masu zanga-zanga musamman a birnin Abuja."
"Faifan bidiyon da ake yadawa ya kai makwanni shida yayin wata ganawa da shugabannin jam'iyyar LP inda NLC ke zanga-zanga."
"A matsayin manyan jam'iyyar, da ni da sanatoci da sauran Mambobin Majalisar Wakilai da Peter Obi mun fita domin kwantar musu da hankali."

Kara karanta wannan

"Babu ruwanmu," Gwamnati ta kare kanta bayan tangardar intanet da rufe layukan waya

- Ireti Kingibe

Sanata Kingibe ta ce a yanzu masu kitsa karairayin sun dawo da tsohon bidiyo domin nuna cewa ita da Peter Obi suna daukar nauyin zanga-zanga.

Wike ya zargi Sanata kan zanga-zanga

Kun ji cewa Ministan Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa an gano wata sanata da ke daukar nauyin masu yin zanga-zanga.

Wike ya bayyana haka yayin taro da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro inda ya ce an gano sanata na ba da abinci ga masu zanga-zanga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.