An Shiga Rana ta 2 na Zanga Zanga, Jama'a Sun Fara Hallara a Garin Tinubu

An Shiga Rana ta 2 na Zanga Zanga, Jama'a Sun Fara Hallara a Garin Tinubu

  • Yau ce rana ta biyu da fara zanga-zangar kwanaki 10 domin adawa da manufofin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu
  • 'Yan Najeriya na ganin manufofin gwamnatin tarayya ne su ka kara jefa su a cikin matsin rayuwa da kuncin talauci
  • An samu tashe-tashen hankula a wasu jihohin Arewacin kasar, amma an fara hallara a Legas domin shiga rana ta biyu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Legas - Duk da yadda aka samu tashe-tashen hankula a jihohin kasar nan saboda zanga-zanga, jama'a sun fara taruwa a Legas domin fara tattaki.

Ranar Alhamis aka fara zanga-zangar kwanaki 10 wacce ake sa ran za ta nunuwa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu cewa ana jin jiki a kasar nan.

Kara karanta wannan

"Babu ruwanmu," Gwamnati ta kare kanta bayan tangardar intanet da rufe layukan waya

Anadolu Agency
An fara shirin zanga-zanga rana ta 2 a Legas Hoto: Anadolu Agency
Asali: Facebook

Jaridar The Nation ta tattara cewa yanzu haka masu zanga-zanga sun shirya ci gaba da tattakinsu, an fara taruwa a Gani Fawehinmi Freedom Park, Ojota, Legas.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ana sa ran idan an kammala taruwa, za a ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana domin neman sauƙin matsin rayuwa da ake ciki.

An tsaurara tsaro gabanin zanga-zanga

An hango dandazon jami'an tsaro jibge tare da jama'a a kwana na biyu da fara gudanar da zanga-zanga.

An ji jami'an tsaron su na kokarin nusar da jama'a cewa kar su rufe hanyoyi su tayar da hatsaniya yayin zanga-zangar rashin jin dadin manufofin gwamnatin tarayya.

Jami'an tsaro sun tabbatar da cewa za su ci gaba da bayar da tsaro ga dukkanin masu fita zanga-zanga matukar sun bi doka.

Zanga-zanga: Gwamnati ta sanya dokar hana fita

A baya mun ruwaito cewa gwamnatin jihar Kano ta ayyana dokar hana fice da shige a fadin jihar na tsawon awanni 24 saboda yadda aka samu matsala yayin zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Bidiyo: Kiristoci sun ba Musulmai masu sallar Juma'a kariya ana tsaka da zanga zanga

Tun da fari, gwamna Abba Kabir Yusuf ya zargi wasu bata-gari da dauko hayar 'yan daba da su hargitsa garin na maimakon gudanar da zanga-zangar lumana da ake shirya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.