“Jami’an Tsaro Sun Gano Sanata Mai Daukar Nauyin Zanga Zanga,” Minista Wike Ya Yi Magana

“Jami’an Tsaro Sun Gano Sanata Mai Daukar Nauyin Zanga Zanga,” Minista Wike Ya Yi Magana

  • An bankado wani sanata da ake zargin yana da hannu wajen ingiza zanga-zangar adawa da gwamnatin Bola Tinubu a fadin kasar
  • Ministan Abuja, Nyesom Wike ne ya bayyana hakan inda ya ce tuni jami’an tsaro suka iya tantance dan majalisar tarayyar
  • Ministan ya kuma yi kira ga masu zanga-zanga a Abuja da su yi biyayya ga umarnin kotu na hana su shiga filin taron Eagles Square

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce hukumomin tsaro sun gano wani sanata da ake zargi da daukar nauyin zanga-zanga a babban birnin kasar.

Ministan ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a Abuja, a ranar Alhamis, 1 ga watan Agusta, bayan wani taro da shugabannin hukumomin tsaro suka yi.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun tarwatsa masu zanga zanga a babban birnin tarayya da Legas

Hukumomin tsaro sun bankado sanatan da ke daukar nauyin zanga-zangar adawa da Tinubu
Wike ya ce an gano sanatan da ke daukar nauyin zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu. Hoto: Nyesom Ezenwo Wike
Asali: Facebook

Legit Hausa ta ruwaito cewa an fara zanga-zangar da aka shirya a jiya Alhamis a Abuja da kuma wasu sassan kasar nan duk da kiran da jami’an gwamnati suka yi na cewa ‘yan kasar su guji zanga-zangar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wanene sanatan? Wike ya yi magana

Nyesom Wike ya ce nan gaba kadan hukumomin tsaro za su gayyaci sanatan domin ya amsa wasu tambayoyi a cewar rahoton jaridar Vanguard.

Ministan Abuja ya ce an fara bin diddigin sanatan ne lokacin da ya dauki rakiyar jami'an tsaro zuwa inda masu zanga-zangar suke tare da raba masu abinci.

“Wani sanata ne ke ba masu zanga-zangar abinci. Idan lokacin ya yi, jami’an tsaro za su gayyaci sanatan, su gano yadda zai rika daukar nauyin bore wa gwamnati mai ci.”

- Nyesom Wike.

Wike ya yi kira ga masu zanga-zanga

Kara karanta wannan

Sanusi II ya yi magana kan zanga zanga, ya fadi hassadar da ake yi wa jihar Kano

Channels TV ya ruwaito minista ya kuma gargadi masu zanga-zangar a babban birnin kasar da su yi biyayya ga umarnin kotu kuma su tsaya a iya filin wasa na MKO Abiola.

A cewar ministan, hukumomin tsaro sun samu rahoton sirri na mutanen da ke son yin garkuwa da zanga-zangar lumana wanda shi ya sa jami'an tsaro ke son masu mutane su tsaya a wuri guda.

An kona hedikwatar APC wajen zanga-zanga

A wani labarin, mun ruwaito cewa fusatattun matasa masu zanga-zanga sun kona hedikwatar jam'iyyar APC ta jihar Jigawa.

An ce lamarin ya faru a yammacin ranar Alhamis bayan da zanga-zangar lumana ta rikide zuwa tashin hankali a Dutse, babban birnin jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.