Ta’addanci a Zanga Zanga: Gwamnan Arewa ya Sanya Dokar Hana Fita ta Awa 24 a Jiharsa

Ta’addanci a Zanga Zanga: Gwamnan Arewa ya Sanya Dokar Hana Fita ta Awa 24 a Jiharsa

  • Sakamakon yadda zanga-zangar lumana ta sauya zani zuwa tashin hankali, an sanya dokar hana fita ta awanni 24 a Yobe
  • Gwamnati ta sanar da sanya dokar ne a yau Alhamis bayan ta gano 'yan daba na son lalata wasu kadarorin gwamnatin jihar
  • Kamar yadda sanarwar mai ba gwamnan Yobe shawara kan lamuran tsaro ta nuna, yankuna uku ne wannan dokar ta shafa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Yobe - Gwamnatin jihar Yobe ta sanya dokar hana fita ta sa'o'i 24 a yankunan Potiskum, Gashua da Nguru na jihar.

Gwamnatin jihar ta kafa dokar ta-bacin ne bayan da wasu ‘yan daba suka kwace zanga-zangar da ake yi a jihar da nufin lalata kadarorin gwamnati.

Kara karanta wannan

Jihohin Arewa da aka sanya dokar hana fita ta awa 24 sun kai 4, an samu cikakken bayani

Gwamnatin Yobe ta sanya dokar hana fita ta awanni 24
Gwamnatin Yobe ta sanya dokar hana fita a wasu yankuna uku. Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Yobe: 'Yan daba sun kwace zanga-zanga

Mai ba gwamnan Yobe shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdussallam (mai ritaya) ya sanar da hakan kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar da Birgediya Janar Dahiru Abdussallam ya fitar ta ce:

“Gwamnatin jihar Yobe ta damu matuka kan yanayin tsaro a garuruwan Potiskum, Gashua, da Nguru a wannan lokaci na zanga-zanga.
"Gwamnatin ta gano cewa akwai wasu 'yan daba da suka kwace zanga-zangar lumanar da nufin farwa kadarori da sace dukiyar gwamnati."

Gwamnatin Yobe ta sanya dokar hana fita

Mai ba gwamnan shawara ya ci gaba da cewa:

“Saboda haka, gwamnatin jihar Yobe ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Potiskum, Gashua da Nguru.
Ana shawartar jama’a da su bi dokar hana fita da kuma zama a gida domin samun zaman lafiya a wadannan yankuna da ma jihar baki daya."

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Gwamna Abba ya sanya dokar hana fita a Kano, ya umarci jami'an tsaro

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta ba jami'an tsaro umarnin tabbatar da an bi wannan dokar a yankunan da abin ya shafa.

Gwamna Zulum ya sanya dokar hana fita

A wani labarin makamancin wannan, mun ruwaito cewa Gwamna Babagana Zulum ya sanya dokar hana fita ta awanni 24 a fadin jihar Borno.

Wannan na zuwa ne bayan da wani bam ya tashi a jihar wanda ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutum 16 tare da jikkata mutane da dama.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.