Kungiyar Duniya ta Goyi Bayan 'Yan Zanga Zanga a Najeriya, Ta Taso 'Yan Majalisa a Gaba

Kungiyar Duniya ta Goyi Bayan 'Yan Zanga Zanga a Najeriya, Ta Taso 'Yan Majalisa a Gaba

  • Kwanaki biyu ya rage 'yan kasar nan su fita zanga-zangar lumana a birnin tarayya Abuja da sauran sassan Najeriya
  • Kungiyar Action Aid ta bi sahun wasu kungiyoyi wajen kiran hukumomin tsaro da su kare rayuka da dukiyoyin jama'a a lokacin
  • Kungiyar ta bayyana muhimmancin a kyale 'yan kasar nan su gudanar da zanga-zangar lumana cikin kwanciyar hankali

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Kungiyar da ke rajin kawar da talauci da kare hakkin dan Adam a Najeriya da wasu kasashe 45 na duniya ta Action Aid ta tunatar da hukumomin muhimmancin tsaro.

Action Aid na wannan batu ne a kan masu shirin gudanar da zanga-zangar lumana ta kwanaki 10 a kasar nan.

Kara karanta wannan

'Yan siyasa da kungiyoyi da ke goyon bayan zanga zanga da wadanda suka kushe tsarin

Ahmed
Kungiyar Action Aid ta nemi tsaron rayukan masu zanga-zanga Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Source: Facebook

Jaridar Punch ta wallafa shugaban kungiyar na kasar nan, Andrew Mamedu na cewa duk dan kasa ya na da 'yancin bayyana bacin ransa ta hanyar zanga-zanga ba tare da tsoro ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zanga-zanga: An shawarci gwamnatin tarayya

Kungiyar Action Aid Nigeria ta shawarci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da kar ayi amfani da karfi a kan masu zanga-zanga.

Ana sa ran za a gudanar da zanga-zangar lumana daga ranar Alhamis, 1 Agusta 2024 har zuwa 10 ga wata domin adawa da manufofin gwamnatin Tinubu.

An fadi matakin magance zanga-zanga

Shugaban kungiyar Action Aid na Najeriya, Andrew Mamedu ya bayyana cewa kamata ya yi gwamnatin tarayya ta magance koken masu zanga-zanga.

Mista Mamedu ya bukaci 'yan majalisar tarayya su daina karbar alawus-alawus ba wai kawai rage albashi ba, Vanguard ta wallafa.

Kara karanta wannan

Baraka ta shiga kungiyar yarbawa a kan zanga zangar adawa da manufofin Tinubu

Idan aka rage kudin da ake biyan 'yan majalisar dattawa da wakilan tarayya, kungiyar ta na ganin za a iya magance wahalhalun talakawan Najeriya.

Matasa sun yi tattakin watsi da zanga-zanga

A wani rahoton kun ji yadda wasu matasa a jihar Legas su ka yi tattaki su na shawarartar jama'a su yi watsi da fita zanga-zanga a farkon watan Agusta.

Matasan da su ka taru a Lagos Island sun ce har yanzu ana jin illar zanga-zangar EndSARS, saboda haka bai kamata a maimaita irin wannan a bana ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng