Kungiyar Duniya ta Goyi Bayan 'Yan Zanga Zanga a Najeriya, Ta Taso 'Yan Majalisa a Gaba

Kungiyar Duniya ta Goyi Bayan 'Yan Zanga Zanga a Najeriya, Ta Taso 'Yan Majalisa a Gaba

  • Kwanaki biyu ya rage 'yan kasar nan su fita zanga-zangar lumana a birnin tarayya Abuja da sauran sassan Najeriya
  • Kungiyar Action Aid ta bi sahun wasu kungiyoyi wajen kiran hukumomin tsaro da su kare rayuka da dukiyoyin jama'a a lokacin
  • Kungiyar ta bayyana muhimmancin a kyale 'yan kasar nan su gudanar da zanga-zangar lumana cikin kwanciyar hankali

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Kungiyar da ke rajin kawar da talauci da kare hakkin dan Adam a Najeriya da wasu kasashe 45 na duniya ta Action Aid ta tunatar da hukumomin muhimmancin tsaro.

Kara karanta wannan

'Yan siyasa da kungiyoyi da ke goyon bayan zanga zanga da wadanda suka kushe tsarin

Action Aid na wannan batu ne a kan masu shirin gudanar da zanga-zangar lumana ta kwanaki 10 a kasar nan.

Ahmed
Kungiyar Action Aid ta nemi tsaron rayukan masu zanga-zanga Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Jaridar Punch ta wallafa shugaban kungiyar na kasar nan, Andrew Mamedu na cewa duk dan kasa ya na da 'yancin bayyana bacin ransa ta hanyar zanga-zanga ba tare da tsoro ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zanga-zanga: An shawarci gwamnatin tarayya

Kungiyar Action Aid Nigeria ta shawarci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da kar ayi amfani da karfi a kan masu zanga-zanga.

Ana sa ran za a gudanar da zanga-zangar lumana daga ranar Alhamis, 1 Agusta 2024 har zuwa 10 ga wata domin adawa da manufofin gwamnatin Tinubu.

An fadi matakin magance zanga-zanga

Shugaban kungiyar Action Aid na Najeriya, Andrew Mamedu ya bayyana cewa kamata ya yi gwamnatin tarayya ta magance koken masu zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Baraka ta shiga kungiyar yarbawa a kan zanga zangar adawa da manufofin Tinubu

Mista Mamedu ya bukaci 'yan majalisar tarayya su daina karbar alawus-alawus ba wai kawai rage albashi ba, Vanguard ta wallafa.

Idan aka rage kudin da ake biyan 'yan majalisar dattawa da wakilan tarayya, kungiyar ta na ganin za a iya magance wahalhalun talakawan Najeriya.

Matasa sun yi tattakin watsi da zanga-zanga

A wani rahoton kun ji yadda wasu matasa a jihar Legas su ka yi tattaki su na shawarartar jama'a su yi watsi da fita zanga-zanga a farkon watan Agusta.

Matasan da su ka taru a Lagos Island sun ce har yanzu ana jin illar zanga-zangar EndSARS, saboda haka bai kamata a maimaita irin wannan a bana ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.