Zanga Zanga: Peter Obi Ya Barranta da Kwankwaso, Ya Fadi Masu Daukar Nauyinta

Zanga Zanga: Peter Obi Ya Barranta da Kwankwaso, Ya Fadi Masu Daukar Nauyinta

  • Dan takarar shugaban kasar Najeriya a zaben 2023, Peter Obi ya fadi matsayarsa kan shriin zanga-zanga da matasa ke yi
  • Obi ya bayyana cewa hakkinsu ne na 'yan kasa su gudanar da zanga-zanga kamar yadda kundin tsarin mulki ya ba su dama a Najeriya
  • Jigon jam'iyyar LP ya ce ya kamata shugabanni su yi gaggawar kawo mafita a Najeriya duba da halin kunci da ake ciki a kasar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Abia - Dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter Obi ya yi magana kan shirin zanga-zanga a Najeriya.

Peter Obi ya goyi bayan zanga-zangar inda ya ce hakkin 'yan kasa ne gudanar da ita cikin lumana ba tare da rigima ba.

Kara karanta wannan

"Rashin cin zabe ne": Ministan Tinubu ya tona asirin wadanda ke shirya zanga zanga

Peter Obi ya fadi matsayarsa kan zanga-zanga sabanin Kwankwaso
Peter Obi ya goyi bayan zanga-zanga sabanin fahimtar Rabiu Kwankwaso. Hoto: Peter Obi.
Asali: Facebook

Zanga-zanga: Peter Obi ya fadi matsayarsa

Tsohon gwamnan Anambra ya bayyana haka ne a cikin wani bidiyo da Channels TV ta wallafa a yau Lahadi 28 ga watan Yulin 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Obi ya ce babu masu daukar nauyin zanga-zangar illa yunwa da da rashin tabbas kan makomar kasar da kuma talauci.

"Idan suna maganar masu daukar nauyin zanga-zanga, ce musu na ke ai amsar mai sauki ce, yunwa ne da rashin tabbas tsakanin matasa."

- Peter Obi

Obi ya shawarci jami'an tsaro kan zanga-zanga

Peter Obi ya ce hakan shi zai tabbatarwa da shugabanni cewa matasa suna dauke da korafi duba da halin da ake ciki a yanzu.

Tsohon dan takarar ya ce tabbas babu wanda ya isa a yanzu ya ce ba a cikin matsanancin halin kunci a kasar baki daya.

Ya bukaci jami'an tsaro da su ba masu zanga-zangar kariya domin gudanar da ita cikin lumana ba tare da matsala ba.

Kara karanta wannan

"Talauci ne ke damunku": Fitaccen mawaki ya soki masu shirin zanga zanga

Kwanwkaso ya shawarci matasa masu zanga-zanga

Mun kawo muku labarin cewa Sanata Rabiu Kwanwkaso ya magantu kan shirin zanga-zanga da matasa ke yi a Najeriya.

Kwanwkaso karara ya nuna cewa zanga-zanga ba ita ba ce mafita inda ya tabbatar da cewa ana cikin wani hali a kasar.

Sanatan ya ce ya kamata mutane su yi amfani ne da akwatin zabe wurin kawar da azzaluman shugabanni da suka saka jama'a a kunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.